< 2 Tarihi 13 >

1 A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
Torej v osemnajstem letu kralja Jerobeáma, je nad Judom začel kraljevati Abíja.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
Tri leta je kraljeval v Jeruzalemu. Ime njegove matere je bilo Mihajá, Uriélova hči iz Gíbee. In bila je vojna med Abíjem in Jerobeámom.
3 Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
Abíja se je postrojil z vojsko hrabrih bojevnikov, celó štiristo tisoč izbranih mož. Tudi Jerobeám se je postrojil zoper njega z osemsto tisoč izbranimi možmi, ki so bili močni junaški možje.
4 Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
Abíja je stal na gori Cemarájim, ki je na gori Efrájim in rekel: »Poslušaj me, ti Jerobeám in ves Izrael,
5 Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
ne veste, da je Gospod, Izraelov Bog, dal kraljestvo nad Izraelom Davidu na veke, celó njemu in njegovim sinovom s solno zavezo?
6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
Vendar je Nebátov sin Jerobeám, služabnik Davidovega sina Salomona, vstal in se uprl zoper svojega gospoda.
7 sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
In k njemu so bili zbrani praznoglavi možje, Beliálovi otroci in so se okrepili zoper Salomonovega sina Rehabáma, ko je bil Rehabám mlad in nežnega srca in se jim ni mogel zoperstaviti.
8 “Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
In sedaj se vi mislite zoperstaviti Gospodovemu kraljestvu v roki Davidovih sinov. Vas je velika množica in tam sta z vami zlati teleti, katera vam je Jerobeám naredil za bogova.
9 Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
Mar niste vrgli ven Gospodove duhovnike, Aronove sinove in Lévijevce in ste si naredili duhovnike po načinu narodov drugih dežel? Tako da kdorkoli prihaja, da sebe umésti z mladim bikcem in sedmimi ovni, isti lahko postane duhovnik tistim, ki so ne-bogovi.
10 “Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
Toda kar se nas tiče, je Gospod naš Bog in mi ga nismo zapustili, in duhovniki, ki služijo Gospodu, so Aronovi sinovi in Lévijevci čakajo na svoj posel.
11 Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
Vsako jutro in vsak večer Gospodu zažigajo žgalne daritve in dišeče kadilo. Tudi hlebe navzočnosti postavljajo na čisto mizo in zlati svečnik z njegovimi svetilkami prižigajo vsak večer. Kajti mi se držimo naročila Gospoda, našega Boga, toda vi ste ga zapustili.
12 Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
Glejte, sam Bog je z nami za našega poveljnika in njegovi duhovniki z donenjem trobent, da zoper vas zatrobijo alarm. Oh Izraelovi otroci, ne borite se zoper Gospoda, Boga svojih očetov, kajti ne boste uspeli.«
13 To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
Toda Jerobeám je velel zasedi, da pride naokrog za njimi. Tako so bili pred Judom in zaseda je bila za njimi.
14 Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
Ko je Juda pogledal nazaj, glej, bitka je bila spredaj in zadaj. Zavpili so h Gospodu in duhovniki so zatrobili s trobentami.
15 mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
Potem so možje iz Juda zakričali in ko so možje iz Juda zakričali, se je pripetilo, da je Bog udaril Jerobeáma in ves Izrael pred Abíjem in Judom.
16 Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
Izraelovi otroci so pobegnili pred Judom in Bog jih je izročil v njihovo roko.
17 Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
Abíja in njegovo ljudstvo jih je umorilo z velikim pokolom. Tako so tam padli umorjeni Izraelci, petsto tisoč izbranih mož.
18 Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Tako so bili Izraelovi otroci ob tistem času podjarmljeni, Judovi otroci pa so prevladali, ker so se zanašali na Gospoda, Boga svojih očetov.
19 Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
Abíja je zasledoval Jerobeáma in od njega vzel mesta: Betel z njegovimi mesti, Ješáno z njenimi mesti in Efrón z njegovimi mesti.
20 Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
Niti ni Jerobeám ponovno obnovil moči v Abíjevih dneh, in Gospod ga je udaril in je umrl.
21 Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
Toda Abíja je postal mogočen in poročil štirinajst žena ter zaplodil dvaindvajset sinov in šestnajst hčera.
22 Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.
Ostala Abíjeva dela, njegove poti in njegove besede so zapisane v zgodbi preroka Idója.

< 2 Tarihi 13 >