< 2 Tarihi 13 >

1 A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
در هجدهمین سال سلطنت یربعام پادشاه اسرائیل، ابیا پادشاه یهودا شد و سه سال در اورشلیم سلطنت کرد. مادرش معکه دختر اوری‌ئیل جِبعه‌ای بود. بین ابیا و یربعام جنگ درگرفت.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
3 Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
سپاه یهودا که از ۴۰۰٬۰۰۰ مرد جنگی و کارآزموده تشکیل شده بود به فرماندهی ابیای پادشاه به جنگ سپاه اسرائیل رفت که تعداد آن دو برابر سپاه یهودا بود و افرادش همه سربازانی کارآزموده و قوی بودند و فرماندهی آنها را یربعام پادشاه به عهده داشت.
4 Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
وقتی دو لشکر در کوهستان افرایم به همدیگر رسیدند، ابیای پادشاه از کوه صمارایم بالا رفته و با صدای بلند به یربعام پادشاه و لشکر اسرائیل گفت:
5 Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
«به من گوش دهید! مگر نمی‌دانید که خداوند، خدای اسرائیل عهد ابدی با داوود بسته است که پسران او همیشه بر اسرائیل سلطنت کنند؟
6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
پادشاه شما یربعام، غلام سلیمان پسر داوود بود و به ارباب خود خیانت کرد.
7 sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
عده‌ای از اراذل و اوباش دور او جمع شدند و بر ضد رحبعام، پسر سلیمان شورش کردند. رحبعام چون جوان و کم‌تجربه بود، نتوانست در برابر آنها ایستادگی کند.
8 “Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
حال خیال می‌کنید می‌توانید سلطنت خداوند را که در دست فرزندان داوود است، سرنگون کنید؟ لشکر شما بزرگ است و گوساله‌های طلا را که یربعام برای پرستش ساخته است نیز نزد شماست.
9 Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
شما کاهنان خداوند را که از نسل هارون هستند و لاویان را از میان خود رانده و مانند مردمان سرزمینهای دیگر، کاهنان بت‌پرست برای خویش تعیین کرده‌اید. هر کسی را که با یک گوساله و هفت قوچ برای کاهن شدن نزد شما بیاید، او را به عنوان کاهن بتهایتان قبول می‌کنید.
10 “Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
«ولی خداوند، خدای ماست و ما او را ترک نکرده‌ایم. کاهنان ما که خداوند را خدمت می‌کنند از نسل هارون هستند و لاویان نیز آنها را در انجام وظیفه‌ای که دارند یاری می‌کنند.
11 Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
آنها هر روز صبح و عصر قربانیهای سوختنی و بخور معطر به خداوند تقدیم می‌کنند و نان حضور را روی میز مخصوص می‌گذارند. هر شب چراغدان طلا را روشن می‌کنند. ما دستورهای خداوند، خدای خود را اطاعت می‌کنیم، ولی شما، او را ترک نموده‌اید.
12 Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
خدا با ماست و او رهبر ماست. کاهنان خدا با نواختن شیپور، ما را برای جنگ با شما رهبری خواهند کرد. ای مردم اسرائیل بر ضد خداوند، خدای اجدادتان نجنگید، زیرا پیروز نخواهید شد.»
13 To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
در این ضمن، یربعام قسمتی از نیروهای خود را فرستاد تا از پشت سر به نیروهای یهودا حمله کنند و خود با بقیهٔ لشکر از روبرو به آنها حمله کرد.
14 Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
لشکر یهودا وقتی دیدند دشمن از پس و پیش آنها را محاصره کرده است، به سوی خداوند دعا کردند و کاهنان شیپورها را نواختند.
15 mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
مردان یهودا شروع کردند به فریاد زدن. وقتی آنها فریاد می‌زدند، خدا ابیای پادشاه و مردان یهودا را یاری کرد تا یربعام و لشکر اسرائیل را تار و مار کرده، شکست دهند.
16 Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
17 Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
آنها در آن روز ۵۰۰٬۰۰۰ سرباز اسرائیلی را کشتند.
18 Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
به این ترتیب، یهودا با اتکاء و اعتماد بر خداوند، خدای اجداد خود، اسرائیل را شکست داد.
19 Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
ابیا به تعقیب یربعام پرداخت و از شهرهای او بیت‌ئیل، یشانه، افرون و روستاهای اطراف آنها را گرفت.
20 Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
یربعام، پادشاه اسرائیل در تمام عمر ابیا دیگر هرگز به قدرت نرسید و سرانجام خداوند او را کشت.
21 Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
اما ابیا قویتر می‌شد. او چهارده زن و بیست و دو پسر و شانزده دختر داشت.
22 Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.
شرح بقیه رویدادهای دوران سلطنت ابیا و کردار و گفتار او در کتاب تاریخ عدوی نبی نوشته شده است.

< 2 Tarihi 13 >