< 2 Tarihi 13 >

1 A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
I kong Jeroboams attende år blev Abia konge over Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
Han regjerte tre år i Jerusalem. Hans mor hette Mikaja; hun var datter av Uriel og var fra Gibea. Mellem Abia og Jeroboam var det krig.
3 Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
Abia begynte krigen med en hær av djerve stridsmenn, fire hundre tusen utvalgte menn; men Jeroboam stilte sig i fylking mot ham med åtte hundre tusen utvalgte menn, også djerve stridsmenn.
4 Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
Abia gikk op på fjellet Semara'im, som hører til Efra'im-fjellene, og trådte frem og sa: Hør på mig, Jeroboam og hele Israel!
5 Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
Skulde I ikke vite at Herren, Israels Gud, har gitt David kongedømmet over Israel til evig tid, ham og hans sønner, ved en saltpakt?
6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
Men Jeroboam, Nebats sønn, Salomos, Davids sønns tjener, gjorde oprør mot sin herre.
7 sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
Og det samlet sig om ham en flokk løse folk og onde mennesker, og de satte sig med vold op imot Rehabeam, Salomos sønn; og Rehabeam var ung og motløs og kunde ikke stå sig mot dem.
8 “Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
Og nu tenker I at I kan stå eder mot Herrens kongedømme, som Davids sønner har i hende, fordi I er en stor hop og har hos eder de gullkalver som Jeroboam lot gjøre forat de skulde være eders guder.
9 Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
Har I ikke jaget bort Herrens prester, Arons sønner, og levittene og selv gjort eder prester, som folkene i hedningelandene gjør? Hver den som kommer med en ung okse og syv værer for å fylle sin hånd, han blir prest for disse guder som ikke er guder.
10 “Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
Men vår Gud er Herren; vi har ikke forlatt ham, og sønner av Aron tjener Herren som prester, og levittene utfører sitt arbeid;
11 Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
hver morgen og aften brenner de brennoffer og velluktende røkelse for Herren og legger frem skuebrød på bordet av rent gull og holder gull-lysestaken og dens lamper i stand og tender den hver aften; vi tar vare på hvad Herren vår Gud vil ha varetatt, men I har forlatt ham.
12 Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
Sannelig, Gud er med oss, han er vår fører, og vi har hans prester med larmtrompetene for å blåse til strid mot eder. I Israels barn, strid ikke mot Herren, eders fedres Gud! For det vil ikke lykkes for eder!
13 To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
Men Jeroboam lot et bakhold dra omkring for å komme bak på dem, så de selv var foran Judas menn, og bakholdet i ryggen på dem.
14 Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
Og da Judas menn vendte sig om, fikk de se fienden både foran sig og bak sig; da ropte de til Herren, og prestene blåste i trompetene.
15 mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
Og Judas menn opløftet krigsrop; da skjedde det, at med det samme Judas menn opløftet krigsropet, da lot Gud Jeroboam og hele Israel bli slått av Abia og Juda.
16 Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
Israels barn flyktet for Juda, og Gud gav dem i deres hånd.
17 Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
Og Abia og hans folk voldte et stort mannefall iblandt dem, og det falt fem hundre tusen utvalgte menn av Israel.
18 Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Således blev Israels barn dengang ydmyket; men Judas barn blev sterke, fordi de satte sin lit til Herren, sine fedres Gud.
19 Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
Abia forfulgte Jeroboam og tok fra ham byene Betel med tilhørende småbyer og Jesana med tilhørende småbyer og Efron med tilhørende småbyer.
20 Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
Jeroboam maktet ikke mere noget så lenge Abia levde, og Herren slo ham så han døde.
21 Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
Men Abia blev mektig. Han tok sig fjorten hustruer og fikk to og tyve sønner og seksten døtre.
22 Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.
Hvad som ellers er å fortelle om Abia, om hans ferd og hans foretagender, det er opskrevet i profeten Iddos historiebok.

< 2 Tarihi 13 >