< 2 Tarihi 13 >

1 A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
When Jeroboam had been ruling [Israel] for almost 18 years, Abijah became the king of Judah.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
He ruled in Jerusalem for three years. His mother was Micaiah (OR, Maacah), the daughter of Uriel from Gibeah [town]. There was a war between [the armies of] Abijah and Jeroboam.
3 Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
Abijah went into the battle, taking 400,000 of his capable soldiers, and Jeroboam prepared to fight them, taking 800,000 of his capable troops.
4 Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
Abijah stood on the top of Zemaraim Mountain, which is in the hilly area that belonged to the tribe of Ephraim, and he shouted, “Jeroboam and all you other people of Israel, listen to me!
5 Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
You should know that Yahweh, the God to whom all we Israelis belong, has appointed David and his descendants to be the kings of Israel forever. He has confirmed that by making a permanent agreement.
6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
But Jeroboam, who was [only] an official of David’s son King Solomon, rebelled against his king.
7 sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
And when Solomon’s son Rehoboam became king and was still young and inexperienced, a group of worthless scoundrels gathered around you, Jeroboam, and rebelled against Rehoboam.
8 “Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
“And now you are planning to fight against the kingdom that Yahweh established to be governed by David’s descendants. It is true that you have a huge army, and you and your soldiers have brought with you the golden [statues of] calves that Jeroboam’s workers made to be gods for all of you.
9 Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
But you expelled the priests that Yahweh [appointed], men who are descendants of Aaron [the first Supreme Priest], and you expelled the descendants of Levi, and you appointed the priests that you wanted, like the people of other countries do. You allow anyone to become a priest of idols that are not gods if he comes to dedicate himself to be a priest by sacrificing a young bull and seven rams.
10 “Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
“As for us, Yahweh is our God, and we have not abandoned him. Our priests who serve Yahweh are descendants of Aaron, and the descendants of Levi assist them.
11 Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
Every morning and every evening they present to Yahweh offerings to be completely burned [on the altar], and they burn fragrant incense. [Each week] they place the sacred bread on the sacred table, and each morning they light the lamps that are on the gold lampstand. We are obeying what Yahweh our God requires us to do. But you have abandoned him.
12 Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
Yahweh is with us; he is our leader. The priests whom he has appointed will blow their trumpets to signal [that we are ready] to fight a battle against you. You Israeli men, do not fight against Yahweh, the God to whom your ancestors belonged, because you will not be successful and win the battle against him.”
13 To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
[While he was speaking, ] Jeroboam sent some of his troops around the army of Judah. So while the soldiers who were with Jeroboam were in front of the army of Judah, the other soldiers of Israel were behind the army of Judah.
14 Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
When the soldiers of Judah turned and saw that they were going to be attacked from the front and from the rear, they cried out to Yahweh. The priests blew their trumpets,
15 mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
and the men of Judah shouted a loud battle-cry. Then Yahweh [enabled Abijah and the army of Judah to] defeat Jeroboam and [the army of] Israel.
16 Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
The soldiers of Israel fled from the soldiers of Judah, and God enabled the army of Judah to defeat them.
17 Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
Abijah and his troops struck the capable soldiers of Israel and killed 500,000 of them.
18 Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
So the soldiers of Israel were defeated, and the soldiers of Judah won the battle because they trusted in Yahweh, the God to whom their ancestors belonged.
19 Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
Abijah’s army pursued the army of Jeroboam, and they captured from the people of Israel the cities of Bethel, Jeshanah, and Ephron, and the surrounding villages.
20 Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
During the remaining time that Abijah ruled, Jeroboam did not become powerful again. Then Yahweh caused him to become very ill, and he died.
21 Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
But Abijah became more powerful. He married 14 wives and had 22 sons and 16 daughters.
22 Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.
An account of the other things that Abijah did while he was the king, including what he said and what he did, is in the scroll written by the prophet Iddo.

< 2 Tarihi 13 >