< 2 Tarihi 13 >

1 A shekara ta sha takwas ta sarautar Yerobowam, Abiya ya zama sarkin Yahuda,
I Kong Jerobeams attende Regeringsår blev Abija Konge over Juda.
2 ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru uku. Sunan mahaifiyarsa Mikahiya ce,’yar Uriyel na Gibeya. Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Abiya da Yerobowam.
Tre År herskede han i Jerusalem. Hans Moder hed Mikaja og var Datter af Uriel fra Gibea. Abija og Jeroboam lå i Krig med hinanden.
3 Abiya ya tafi yaƙi tare da mayaƙa dubu ɗari huɗu jarumawa, Yerobowam kuwa ya ja dāgār yaƙi a kan Abiya da mayaƙa dubu ɗari takwas jarumawa.
Abija åbnede Krigen med en krigsdygtig Hær, 400.000 udsøgte Mænd, og Jeroboam mødte ham med 800.000 udsøgte Mænd, dygtige Krigere,
4 Abiya ya tsaya a Dutsen Zemarayim, a ƙasar tudu ta Efraim ya ce, “Yerobowam da dukan Isra’ila, ku saurare ni!
Da stillede Abija sig på Bjerget Zemarajim, der hører til Efraims Bjerge, og sagde: "Hør mig, Jeroboam og hele Israel!
5 Ba ku san cewa Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ba da sarautar Isra’ila ga Dawuda da zuriyarsa har abada ta wurin alkawarin gishiri ba?
Burde I ikke vide, at HERREN, Israels Gud, har givet David og hans Efterkommere Kongemagten over Israel til evig Tid ved en Saltpagt?
6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, ma’aikacin Solomon ɗan Dawuda, ya tayar wa maigidansa,
Men Jeroboam, Nebats Søn, Davids Søn Salomos Træl, rejste sig og gjorde Oprør mod sin Herre,
7 sai ya tara wa kansa’yan iska da mugayen mutane suka yi gāba da Rehobowam ɗan Solomon. Rehobowam lokacin kuwa ba shi da wayo, don haka bai iya tsai da su ba.
og dårlige Folk, Niddinger, samlede sig om ham og bød Rehabeam, Salomos Søn, Trods; og Rebabeam var ung og veg og kunde ikke hævde sig over for dem.
8 “Yanzu kuna shirin yin tsayayya da mulkin Ubangiji, wanda yake a hannuwan zuriyar Dawuda. Tabbatacce ku ƙasaitacciyar mayaƙa ne kuma kuna tare da ku maruƙan zinariyar da Yerobowam ya yi domin su zama allolinku.
Og nu mener I at kunne hævde eder over for HERRENs Kongedømme i Davids Efterkommeres Hånd, fordi I er en stor Hob og på eders Side har de Guldkalve, Jeroboam lod lave eder til Guder!
9 Ba ku ne kuka kori firistocin Ubangiji,’ya’yan Haruna maza, da Lawiyawa kuka kuma zaɓi firistocinku kamar yadda sauran al’ummai suke yi ba? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don yă tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba.
Har I ikke drevet HERRENs Præster, Arons Sønner, og Leviterne bort og skaffet eder Præster på samme Måde som Hedningefolkene? Enhver, der kommer med en ung Tyr og syv Vædre for at indsættes, bliver Præst for Guder, der ikke er Guder!
10 “Gare mu kuwa, Ubangiji shi ne Allah, kuma ba mu yashe shi ba. Firistocin da suke bauta wa Ubangiji’ya’yan Haruna maza ne, Lawiyawa ne kuwa suke taimakonsu.
Men vor Gud er HERREN, og vi har ikke forladt ham; de Præster, der tjener HERREN, er Arons Sønner og Leviterne udfører den øvrige Tjeneste;
11 Kowace safiya da kowace yamma sukan miƙa hadayun ƙonawa da turare mai ƙanshi ga Ubangiji. Sukan shirya burodi a tsarkaken tebur mai tsabta, sukan kuma ƙuna fitilu a alkukai kowace yamma. Muna kiyaye ƙa’idodin Ubangiji Allahnmu. Amma ku kun yashe shi.
de antænder hver Morgen og Aften Brændofre til HERREN og vellugtende Røgelse, lægger Skuebrødene til Rette på Guldbordet og tænder Guldlysestagen og dens Lamper Aften efter Aften, thi vi holder HERREN vor Guds Forskrifter, men l har forladt ham!
12 Allah yana tare da mu; shi ne shugabanmu. Firistocinsa tare da ƙahoni za su busa kirarin yaƙi a kanku. Mutanen Isra’ila, kada ku yi yaƙi da Ubangiji Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.”
Se, med os, i Spidsen for os er Gud og hans Præster og Alarmtrompeterne, med hvilke der skal blæses til Kamp imod eder! Israeliter, indlad eder ikke i Kamp med HERREN, eders Fædres Gud, thi I får ikke Lykken med eder!"
13 To, fa, Yerobowam ya aiki mayaƙa su zagaya daga baya, domin yayinda yake a gaban Yahuda, sai’yan kwanto su kasance a bayansu.
Jeroboam lod imidlertid Bagholdet gøre en omgående Bevægelse for at komme i Ryggen på dem, og således havde Judæerne Hæren foran sig og Bagholdet i Ryggen.
14 Yahuda ya juya sai ya ga cewa ana yaƙe su gaba da baya. Sai suka yi kuka ga Ubangiji. Firistoci suka busa ƙahoni
Da Judæerne vendte sig om og så, at Angreb truede dem både forfra og bagfra, råbte de til HERREN, medens Præsterne blæste i Trompeterne.
15 mutanen Yahuda kuwa suka tā da kirarin yaƙi. Da ji kirarin yaƙi, Allah ya fatattake Yerobowam da dukan Isra’ila a gaban Abiya da Yahuda.
Så udstødte Judæerne Krigsskriget, og da Judæerne udstødte Krigsskriget, slog Gud Jeroboam og hele Israel foran Abija og Juda.
16 Isra’ilawa suka gudu a gaban Yahuda, Allah kuwa ya bashe su a hannuwansu.
Israeliterne flygtede for Judæerne, og Gud gav dem i deres Hånd;
17 Abiya da mutanensa suka kashe su sosai, har mutum dubu ɗari biyar suka mutu a cikin jarumawan Isra’ila.
og Abija og hans Folk tilføjede dem et stort Nederlag, så der af Israeliterne faldt 500.000 udsøgte Krigere.
18 Aka cinye mutanen Isra’ila a wannan lokaci, mutanen Yahuda kuwa suka yi nasara domin sun dogara ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Således ydmygedes Israeliterne den Gang, men Judæerne styrkedes, fordi de støttede sig til HERREN, deres Fædres Gud.
19 Abiya ya kori Yerobowam ya kuma ƙwace garuruwan Betel, Yeshana da Efron, tare da ƙauyukan da suke kewaye daga gare shi.
Og Abija forfulgte Jeroboam og fratog ham flere Byer, Betel med Småbyer, Jesjana med Småbyer og Efrajin med Småbyer.
20 Yerobowam bai sāke yin ƙarfi a zamanin Abiya ba. Ubangiji ya buge shi ya kuma mutu.
Jeroboam kom ikke til Kræfter mere, så længe Abija levede; og HERREN slog ham, så han døde.
21 Amma Abiya ya ƙara ƙarfi. Ya auri mata goma sha huɗu, ya kuma kasance da’ya’ya maza ashirin da biyu da kuma’ya’ya mata goma sha shida.
Men Abijas Magt voksede. Han ægtede fjorten Hustruer og avlede to og tyve Sønner og seksten Døtre.
22 Sauran ayyukan sauratar Abiya, abin da ya yi da abin da ya faɗa, a rubuce suke a cikin rubuce-rubucen annabi Iddo.
Hvad der ellers er at fortælle om Abija, hans Færd og Ord, står jo optegnet i Profeten Iddos Udlægning".

< 2 Tarihi 13 >