< 2 Tarihi 12 >
1 Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
And it came to pass, when Rehobo'am had established the kingdom, and when he had become strong, that he forsook the law of the Lord, and all Israel with him.
2 Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
And it came to pass in the fifth year of king Rehobo'am, that Shishak the king of Egypt came up against Jerusalem, —because they had acted faithlessly against the Lord, —
3 Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
With twelve hundred chariots and sixty thousand horsemen: and innumerable were the people that came with him out of Egypt—the Lubim, the Sukkiyim, and the Ethiopians.
4 ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
And he captured the fortified cities which pertained to Judah, and he came as far as Jerusalem.
5 Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
And Shem'ayah the prophet came to Rehobo'am, and the princes of Judah, that were gathered together to Jerusalem because of Shishak, and said unto them, Thus hath said the Lord, Ye have indeed forsaken me, and therefore have I also relinquished you into the hand of Shishak.
6 Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
Thereupon the princes of Israel and the king humbled themselves; and they said, The Lord is righteous.
7 Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
And when the Lord saw that they had humbled themselves, then came the word of the Lord to Shem'ayah, saying, “They have humbled themselves: I will not destroy them; but I will permit some little to escape from them; and my wrath shall not be poured out over Jerusalem by the hand of Shishak.”
8 Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
However they shall be servants unto him, and they shall know my service, and the service of the kingdoms of the [various] countries.
9 Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
And so came up Shishak the king of Egypt against Jerusalem, and he took away the treasures of the house of the Lord, and the treasures of the king's house: every thing did he take away; and he took away the shields of gold which Solomon had made.
10 Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
And king Rehobo'am made in their stead shields of copper, and committed them for keeping into the hand of the chiefs of the runners, who kept guard at the door of the king's house.
11 Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
And it happened whenever the king went into the house of the Lord, that the runners came and bore them, and carried them back into the apartment of the runners.
12 Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
And when he had humbled himself, the wrath of the Lord turned from him, so that he destroyed him not to make an end [of him]: and also in Judah were some good things [found].
13 Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
And king Rehobo'am strengthened himself in Jerusalem, and reigned; for Rehobo'am was one and forty years old when he became king, and seventeen years did he reign in Jerusalem, the city which the Lord had chosen out of all the tribes of Israel, to put his name there. And his mother's name was Na'amah the 'Ammonitess.
14 Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
And he did the evil; because he directed not his heart to seek the Lord.
15 Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
And the acts of Rehobo'am, the first and the last, behold, they are written in the history of Shem'ayah the prophet, and of 'Iddo, the seer concerning the genealogies. And the wars of Rehobo'am and Jerobo'am [lasted] all the days.
16 Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.
And Rehobo'am slept with his fathers, and was buried in the city of David: and Abiyah his son became king in his stead.