< 2 Tarihi 12 >

1 Bayan mulkin Rehobowam ya kahu kamar sarki ya kuma yi ƙarfi, shi da dukan Isra’ila suka yi biris da dokar Ubangiji.
And when the kingdom of Rehoboam had been strengthened and fortified, he abandoned the law of the Lord, and all of Israel with him.
2 Domin sun yi rashin biyayya ga Ubangiji, saboda haka Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima a shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam.
Then, in the fifth year of the reign of Rehoboam, Shishak, the king of Egypt, ascended against Jerusalem (for they had sinned against the Lord)
3 Da kekunan yaƙi dubu ɗaya da ɗari biyu da kuma mahayan dawakai dubu haɗe da mayaƙan Libiyawa, Sukkatawa da kuma Kushawa waɗanda suka wuce ƙidaya suka zo tare da shi daga Masar,
with one thousand two hundred chariots and sixty thousand horsemen. And the common people could not be numbered who had arrived with him from Egypt, namely, the Libyans, and the Troglodytes, and the Ethiopians.
4 ya ci biranen katanga na Yahuda har zuwa Urushalima.
And he seized the most fortified cities in Judah, and he went even to Jerusalem.
5 Sai annabi Shemahiya ya zo wurin Rehobowam da kuma wajen shugabannin Yahuda waɗanda suka taru a Urushalima don tsoron Shishak, ya kuma faɗa musu, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Kun yi biris da ni; saboda haka, yanzu na bashe ku ga Shishak.’”
Then Shemaiah, the prophet, entered to Rehoboam, and to the leaders of Judah who had gathered together in Jerusalem while fleeing from Shishak, and he said to them: “Thus says the Lord: You have abandoned me, and so I have abandoned you into the hand of Shishak.”
6 Shugabannin Isra’ila da sarki suka ƙasƙantar da kansu suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.”
And the leaders of Israel, and the king, being in consternation, said, “The Lord is just.”
7 Sa’ad da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai wannan maganar Ubangiji ta zo wa Shemahiya, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba.
And when the Lord had seen that they were humbled, the word of the Lord came to Shemaiah, saying: “Because they have been humbled, I will not disperse them. And I will give to them a little help, and my fury will not rain down upon Jerusalem by the hand of Shishak.
8 Duk da haka za su zama bayinsa, don su san bambanci tsakanin yin mini bauta da kuma yin wa sarakunan sauran ƙasashe bauta.”
Yet truly, they shall serve him, so that they may know the difference between my servitude, and the servitude of a kingdom of the lands.”
9 Da Shishak sarkin Masar ya yaƙi Urushalima, sai ya kwashi ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan sarki. Ya kwashe kome da kome, har da garkuwoyin zinariyar da Solomon ya yi.
And so Shishak, the king of Egypt, withdrew from Jerusalem, taking up the treasures of the house of the Lord and of the house of the king. And he took away everything with him, even the gold shields that Solomon had made.
10 Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara na mashigin gidan sarki.
In place of these, the king made bronze ones, and he delivered them to the leaders of the shield bearers, who were guarding the vestibule of the palace.
11 Duk sa’ad da sarki ya tafi haikalin Ubangiji, masu tsaron sukan tafi tare da shi, suna riƙe da garkuwoyi, daga baya kuma su mai da su a ɗakin tsaro.
And when the king would enter into the house of the Lord, the shield bearers would arrive and take them, and they would carry them back to their armory.
12 Gama Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, fushin Ubangiji ya bar shi, ba a kuwa hallaka shi ƙaƙaf ba. Tabbatacce an yi’yan abubuwa masu kyau a Yahuda.
Yet truly, because they were humbled, the wrath of the Lord turned away from them, and so they were not utterly destroyed. And indeed, good works were also found in Judah.
13 Sarki Rehobowam ya kafa kansa daram a Urushalima, ya kuma ci gaba a matsayin sarki. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila wanda zai sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama ce, ita mutuniyar Ammon ce.
Therefore, king Rehoboam was strengthened in Jerusalem, and he reigned. He was forty-one years old when he had begun to reign, and he reigned for seventeen years in Jerusalem, the city that the Lord chose out of all the tribes of Israel, so that he might confirm his name there. Now the name of his mother was Naamah, an Ammonite.
14 Ya aikata mugunta domin bai sa zuciyarsa ga neman Ubangiji ba.
But he did evil, and he did not prepare his heart so as to seek the Lord.
15 Game da ayyukan mulkin Rehobowam, daga farko zuwa ƙarshe, ba a rubuce suke a tarihin Shemahiya annabi da Iddo mai gani wanda yake zancen zuriyoyi ba? Aka kasance da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
Truly, the works of Rehoboam, the first and the last, have been written in the books of Shemaiah, the prophet, and of Iddo, the seer, and diligently set forth. And Rehoboam and Jeroboam fought against one another during all their days.
16 Rehobowam ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Abiya ɗansa kuma ya gāje shi a matsayin sarki.
And Rehoboam slept with his fathers, and he was buried in the City of David. And his son, Abijah, reigned in his place.

< 2 Tarihi 12 >