< 2 Tarihi 11 >
1 Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
Et Roboam rentré à Jérusalem assembla la maison de Juda et de Benjamin, cent quatre-vingt mille hommes d'élite faisant le service militaire pour entrer en guerre avec Israël, afin de reconquérir le royaume à Roboam.
2 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
Alors la parole de l'Éternel fut adressée à Semaïa, homme de Dieu, en ces termes:
3 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
Parle à Roboam, fils de Salomon, roi de Juda, et à tous les Israélites de Juda et de Benjamin, en ces termes: Ainsi parle l'Éternel:
4 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
Ne marchez pas et ne vous battez pas contre vos frères, rentrez, chacun dans sa demeure; car c'est de par Moi que cette chose a eu lieu. Et ils obéirent aux paroles de l'Éternel, et renoncèrent à la campagne contre Jéroboam.
5 Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
Et Roboam résidait à Jérusalem, et il édifia des villes en forteresses dans Juda,
6 Betlehem, Etam, Tekowa,
et il éleva Bethléhem et Eitam et Thékôa
7 Bet-Zur, Soko, Adullam,
et Bethtsur et Socho et Adullam
et Gath et Marésa et Ziph
9 Adorayim, Lakish, Azeka,
et Adoraïm et Lachis et Azéca
10 Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
et Tsorea et Ajalon et Hébron situées dans Juda et Benjamin, en villes fortes.
11 Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
Et il donna de la force aux remparts et y plaça des commandants et des provisions de vivres, et d'huile et de vin,
12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
et dans chaque ville des boucliers et des lances, et les rendit très fortes. Et à lui étaient Juda et Benjamin.
13 Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
Et les Prêtres et les Lévites qui étaient dans tout Israël, vinrent de tout son territoire, se ranger de son côté.
14 Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
Car les Lévites abandonnèrent leurs aires et leurs propriétés et passèrent en Juda et à Jérusalem, parce que Jéroboam et ses fils les chassèrent du sacerdoce de l'Éternel,
15 Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
et il s'institua des prêtres pour les tertres et les boucs et les veaux qu'il avait fabriqués.
16 Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Et à leur suite, de toutes les Tribus d'Israël ceux qui portaient leur cœur à chercher l'Éternel, Dieu d'Israël, vinrent à Jérusalem pour sacrifier à l'Éternel, Dieu de leurs pères.
17 Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
Et ils renforcèrent le royaume de Juda, et affermirent Roboam, fils de Salomon, pendant trois ans. Car ils suivirent les errements de David et de Salomon, pendant trois ans.
18 Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
Et Roboam prit pour sa femme Mahelath, fille de Jerimoth, fils de David et d'Abihaïl, fille d'Eliab, fils d'Isaï.
19 Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
Et elle lui enfanta des fils, Jeüs et Semaria et Zaham.
20 Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
Et après il épousa Maacha, fille d'Absalom, et elle lui enfanta Abia et Atthaï et Ziza et Selomith.
21 Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
Et Roboam aimait Maacha, fille d'Absalom, plus que toutes ses femmes et concubines; car il avait pris dix-huit femmes et soixante concubines, et il engendra vingt-huit fils et soixante filles.
22 Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
Et Roboam constitua comme chef Abia, fils de Maacha, comme prince entre ses frères, car c'était en vue de le faire roi.
23 Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.
Et il agit prudemment et distribua de ses fils dans toutes les terres de Juda et de Benjamin, dans toutes les villes fortifiées et leur fournit des denrées en abondance, et fit pour eux la demande d'une multitude de femmes.