< 2 Tarihi 11 >

1 Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
Roboam, étant arrivé à Jérusalem, assembla la maison de Juda et de Benjamin, cent quatre-vingt mille hommes de guerre choisis, pour combattre contre Israël, pour ramener le royaume à Roboam.
2 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
Mais la parole de l'Éternel fut adressée à Shémaeja, homme de Dieu, en ces termes:
3 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
Parle à Roboam, fils de Salomon, roi de Juda, et à tout Israël en Juda et en Benjamin, et dis-leur:
4 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
Ainsi dit l'Éternel: Vous ne monterez point, et vous ne combattrez point contre vos frères; retournez- vous-en, chacun dans sa maison; car ceci vient de moi. Et ils obéirent aux paroles de l'Éternel, et s'en retournèrent, renonçant à marcher contre Jéroboam.
5 Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
Roboam demeura donc à Jérusalem, et il bâtit des villes fortes en Juda.
6 Betlehem, Etam, Tekowa,
Il bâtit Bethléhem, Étam, Thékoa,
7 Bet-Zur, Soko, Adullam,
Beth-Tsur, Soco, Adullam,
8 Gat, Maresha, Zif,
Gath, Marésha, Ziph,
9 Adorayim, Lakish, Azeka,
Adoraïm, Lakis, Azéka,
10 Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
Tsoréa, Ajalon et Hébron, qui étaient en Juda et en Benjamin, et en fit des villes fortes.
11 Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
Il les fortifia, et y mit des gouverneurs et des provisions de vivres, d'huile et de vin,
12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
Et, dans chacune de ces villes, des boucliers et des lances, et il les rendit très fortes. Ainsi Juda et Benjamin furent à lui.
13 Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
Les sacrificateurs et les Lévites, qui étaient dans tout Israël, vinrent de toutes parts se ranger auprès de lui.
14 Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
Car les Lévites abandonnèrent leurs banlieues et leurs propriétés et vinrent en Juda et à Jérusalem, parce que Jéroboam, avec ses fils, les avaient rejetés des fonctions de sacrificateurs à l'Éternel,
15 Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
Et s'était établi des sacrificateurs pour les hauts lieux et les démons, et pour les veaux qu'il avait faits.
16 Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Et à leur suite, de toutes les tribus d'Israël, ceux qui avaient à cœur de chercher l'Éternel, le Dieu d'Israël, vinrent à Jérusalem pour sacrifier à l'Éternel, le Dieu de leurs pères.
17 Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
Et ils fortifièrent le royaume de Juda et affermirent Roboam, fils de Salomon, pendant trois ans; car on suivit les voies de David et de Salomon pendant trois ans.
18 Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
Or Roboam prit pour femme Mahalath, fille de Jérimoth, fils de David, et d'Abichaïl, fille d'Éliab, fils d'Isaï.
19 Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
Elle lui enfanta des fils: Jéush, Shémaria et Zaham.
20 Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
Après elle, il prit Maaca, fille d'Absalom, qui lui enfanta Abija, Atthaï, Ziza et Shélomith.
21 Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
Et Roboam aima Maaca, fille d'Absalom, plus que toutes ses femmes et ses concubines. Car il prit dix-huit femmes et soixante concubines, et il engendra vingt-huit fils et soixante filles.
22 Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
Roboam établit pour chef Abija, fils de Maaca, comme prince entre ses frères; car il voulait le faire roi;
23 Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.
Et il agit prudemment et dispersa tous ses fils dans toutes les contrées de Juda et de Benjamin, dans toutes les villes fortes; il leur donna abondamment de quoi vivre, et demanda pour eux une multitude de femmes.

< 2 Tarihi 11 >