< 2 Tarihi 11 >
1 Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
Lorsque Roboam fut arrivé à Jérusalem, il rassembla la maison de Juda et de Benjamin, cent quatre-vingt mille hommes d'élite qui étaient des guerriers, pour combattre Israël, afin de ramener le royaume à Roboam.
2 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
Mais la parole de Yahvé fut adressée à Shemaya, homme de Dieu, en ces termes:
3 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
« Parle à Roboam, fils de Salomon, roi de Juda, et à tout Israël en Juda et en Benjamin, et dis-leur:
4 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
« Yahvé dit: Vous ne monterez pas, et vous ne combattrez pas vos frères! Chacun retournera dans sa maison, car cette chose est de moi. »" Ils écoutèrent donc les paroles de Yahvé et s'en retournèrent après avoir combattu Jéroboam.
5 Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
Roboam habita à Jérusalem, et il bâtit en Juda des villes pour sa défense.
6 Betlehem, Etam, Tekowa,
Il bâtit Bethléem, Etam, Tekoa,
7 Bet-Zur, Soko, Adullam,
Beth Tsur, Soco, Adullam,
9 Adorayim, Lakish, Azeka,
Adoraïm, Lakis, Azéka,
10 Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
Zorah, Aijalon et Hébron, qui sont des villes fortes en Juda et en Benjamin.
11 Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
Il fortifia les places fortes et y plaça des chefs, avec des provisions de vivres, d'huile et de vin.
12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
Il plaça des boucliers et des lances dans toutes les villes, et les rendit extrêmement fortes. Juda et Benjamin lui appartenaient.
13 Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
Les prêtres et les lévites qui étaient dans tout Israël se tinrent avec lui de tout leur territoire.
14 Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
Car les Lévites quittèrent leurs pâturages et leurs biens, et vinrent en Juda et à Jérusalem; car Jéroboam et ses fils les avaient rejetés, afin qu'ils ne remplissent pas les fonctions de prêtres pour Yahvé.
15 Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
Il établit lui-même des prêtres pour les hauts lieux, pour les idoles de boucs et de veaux qu'il avait faites.
16 Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
Après eux, de toutes les tribus d'Israël, ceux qui avaient mis leur cœur à chercher l'Éternel, le Dieu d'Israël, venaient à Jérusalem pour sacrifier à l'Éternel, le Dieu de leurs pères.
17 Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
Ils renforcèrent le royaume de Juda et affermirent Roboam, fils de Salomon, pendant trois ans, car ils marchèrent trois ans dans la voie de David et de Salomon.
18 Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
Roboam prit une femme pour lui, Mahalath, fille de Jerimoth, fils de David, et d'Abihail, fille d'Eliab, fils de Jessé.
19 Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
Elle lui donna des fils: Jeush, Shemariah et Zaham.
20 Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
Après elle, il prit Maaca, petite-fille d'Absalom, et elle lui enfanta Abija, Attaï, Ziza et Shelomith.
21 Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
Roboam aimait Maaca, petite-fille d'Absalom, plus que toutes ses femmes et ses concubines; il prit dix-huit femmes et soixante concubines, et engendra vingt-huit fils et soixante filles.
22 Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
Roboam nomma Abija, fils de Maaca, chef, prince parmi ses frères, car il avait l'intention de le faire roi.
23 Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.
Il fit preuve de sagesse et dispersa quelques-uns de ses fils dans tous les pays de Juda et de Benjamin, dans toutes les villes fortifiées. Il leur donna de la nourriture en abondance, et il leur chercha beaucoup de femmes.