< 2 Tarihi 11 >
1 Sa’ad da Rehobowam ya iso Urushalima, ya tattara mayaƙa dubu ɗari takwas daga gidan Yahuda da Benyamin, don su yi yaƙi da Isra’ila su sāke mai da mulki wa Rehobowam.
And he came Rehoboam Jerusalem and he called together [the] house of Judah and Benjamin one hundred and eighty thousand chosen [man] maker[s] of war to do battle with Israel to restore the kingdom to Rehoboam.
2 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo ga Shemahiya mutumin Allah.
And it came [the] word of Yahweh to Shemaiah [the] man of God saying.
3 “Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon sarkin Yahuda da kuma dukan Isra’ilawan da suke a Yahuda da Benyamin,
Say to Rehoboam [the] son of Solomon [the] king of Judah and to all Israel in Judah and Benjamin saying.
4 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku. Ku tafi gida kowannenku, gama wannan yi na ne.’” Saboda haka suka yi biyayya ga maganar Ubangiji suka kuma koma daga takawa don yaƙi da Yerobowam.
Thus he says Yahweh not you must go up and not you must do battle with countrymen your return everyone to own house his for from with me it has occurred the thing this and they obeyed [the] words of Yahweh and they turned back from going against Jeroboam.
5 Rehobowam ya zauna a Urushalima ya kuma gina garuruwa don kāriya a cikin Yahuda.
And he dwelt Rehoboam in Jerusalem and he built cities to fortification in Judah.
6 Betlehem, Etam, Tekowa,
And he built Beth-lehem and Etam and Tekoa.
7 Bet-Zur, Soko, Adullam,
And Beth Zur and Socoh and Adullam.
And Gath and Mareshah and Ziph.
9 Adorayim, Lakish, Azeka,
And Adoraim and Lachish and Azekah.
10 Zora, Aiyalon da Hebron. Waɗannan su ne garuruwan katanga a cikin Yahuda da Benyamin.
And Zorah and Aijalon and Hebron which [were] in Judah and in Benjamin cities of fortifications.
11 Ya ƙarfafa kāriyarsu ya kuma sa shugabannin mayaƙa a cikinsu, tare da tanadin abinci, man zaitun da kuma ruwan inabi.
And he strengthened the fortifications and he put in them commanders and supplies of food and oil and wine.
12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen, ya kuma sa suka zama da ƙarfi. Saboda haka Yahuda da Benyamin suka zama nasa.
And [were] in every city and a city body shields and spears and he made strong them to abundance exceedingly and it belonged to him Judah and Benjamin.
13 Firistoci da Lawiyawa daga dukan yankuna ko’ina a Isra’ila suka haɗa kai da shi.
And the priests and the Levites who [were] in all Israel they took their stand at him from all territory their.
14 Lawiyawa suka ma bar makiyayansu da mallakarsu, suka zo Yahuda da Urushalima domin Yerobowam da’ya’yansa maza sun ƙi su a matsayin firistocin Ubangiji.
For they forsook the Levites pasture lands their and property their and they went to Judah and to Jerusalem for he had rejected them Jeroboam and sons his from serving as priests to Yahweh.
15 Yerobowam ya naɗa firistocinsa domin masujadan kan tudu da kuma domin gumakan nan na akuya da maraƙin da ya yi.
And he appointed for himself priests for the high places and for the goats and for the calves which he had made.
16 Waɗanda suke daga kowane kabilar Isra’ila waɗanda suka sa zuciya a kan neman Ubangiji, Allah na Isra’ila, suka bi Lawiyawa zuwa Urushalima don su miƙa hadayu ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
And after them from all [the] tribes of Israel those [who] set heart their to seek Yahweh [the] God of Israel they came Jerusalem to sacrifice to Yahweh [the] God of ancestors their.
17 Suka ƙarfafa mulkin Yahuda suka kuma goyi bayan Rehobowam ɗan Solomon shekaru uku, suna tafiya a hanyoyin Dawuda da Solomon a wannan lokaci.
And they strengthened [the] kingdom of Judah and they strengthened Rehoboam [the] son of Solomon for years three for they walked in [the] way of David and Solomon for years three.
18 Rehobowam ya auri Mahalat,’yar Yerimot ɗan Dawuda wadda Abihayil’yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa.
And he took for himself Rehoboam a wife Mahalath ([the] daughter of *Q(K)*) Jerimoth [the] son of David Abihail [the] daughter of Eliab [the] son of Jesse.
19 Ta haifa masa’ya’ya maza. Yewush, Shemariya da Zaham.
And she bore to him sons Jeush and Shemariah and Zaham.
20 Sa’an nan ya auri Ma’aka’yar Absalom, wadda ta haifa masa Abiya, Attai, Ziza da kuma Shelomit.
And after her he took Maacah [the] daughter of Absalom and she bore to him Abijah and Attai and Ziza and Shelomith.
21 Rehobowam ya ƙaunaci Ma’aka’yar Absalom fiye da sauran matansa da ƙwarƙwaransa. Duka-duka dai ya auri mata goma sha takwas da ƙwarƙwarai sittin, yana da’ya’ya maza ashirin da takwas da’ya’ya mata sittin.
And he loved Rehoboam Maacah [the] daughter of Absalom more than all wives his and concubines his for wives eight-teen he had taken and concubines sixty and he fathered twenty and eight sons and sixty daughters.
22 Rehobowam ya naɗa Abiya ɗan Ma’aka yă zama babba yerima a cikin’yan’uwansa, don dai yă naɗa shi sarki.
And he appointed to the chief Rehoboam Abijah [the] son of Maacah to leader among brothers his for to make king him.
23 Ya yi hikima, ya watsar da waɗansu’ya’yansa a dukan yankunan Yahuda da Benyamin, da kuma a dukan birane masu katanga. Ya ba su tanadi mai yawa ya kuma aurar musu mata masu yawa.
And he acted wisely and he distributed some of all sons his to all [the] lands of Judah and Benjamin to all [the] cities of fortifications and he gave to them food to abundance and he sought a multitude of wives.