< 2 Tarihi 10 >

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ilawa sun je can don su naɗa shi sarki.
Rehabeam drog till Sechem; ty hele Israel var kommen till Sechem, att göra honom till Konung.
2 Da Yerobowam ɗan Nebat ya ji wannan (a lokacin yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon ya tafi), sai ya dawo daga Masar.
Och då Jerobeam, Nebats son, som i Egypten var, dit han för Konung Salomo flydd var, det hörde, kom han igen utur Egypten.
3 Saboda haka suka aika a zo da Yerobowam, sai shi da dukan Isra’ila suka je wurin Rehobowam suka ce masa.
Och de sände bort, och läto kalla honom. Och Jerobeam kom med hela Israel; och de talade med Rehabeam, och sade:
4 “Mahaifinka ya sa mana kaya masu nauyi a kanmu, amma yanzu ka sauƙaƙa mana aiki mai zafin nan da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
Din fader hafver gjort vårt ok allt för hårdt; så lätta du ini dins faders hårda tjenst, och det svåra ok som han på oss lagt hafver, så vilje vi vara dig underdånige.
5 Rehobowam ya amsa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.” Saboda haka mutanen suka watse.
Han sade till dem: Efter tre dagar kommer igen till mig. Och folket gick sin väg.
6 Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawan da suka yi wa mahaifinsa Solomon hidima a lokacin da yake da rai, ya tambaye suya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
Och Konung Rehabeam rådfrågade med de äldsta, som för hans fader Salomo ståndit hade, medan han lefde, och sade: Hvad råden I, det jag skall svara desso folkena?
7 Suka amsa suka ce, “In za ka ji tausayi waɗannan mutane ka kuma gamshe su, ka kuma ba su amsar da ta dace, kullum za su zama bayinka.”
De talade med honom, och sade: Om du ställer dig vänliga till detta folk, och far väl åt dem, och gifver dem god ord, så blifva de dig underdånige i alla sina dagar.
8 Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawa suka ba shi ya kuma nemi shawarar matasan da suka yi girma tare, suke kuma yin masa hidima.
Men han lät blifva de äldstas råd, som de honom gifvit hade, och rådfrågade med de unga, som med honom uppväxte voro, och för honom stodo;
9 Ya tambaye su ya ce, “Mece ce shawararku? Yaya zan amsa wa waɗannan mutanen da suke ce mini, ‘Ka sauƙaƙa nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
Och sade till dem: Hvad råden I, det vi desso folkena svara skole, som med mig talat hafva, och sagt: Lätta oss det ok, som din fader på oss lagt hafver.
10 Matasan da suka yi girma tare shi suka amsa, “Faɗa wa mutanen da suke ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sauƙaƙa nauyinmu.’ Ka faɗa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun mahaifina kauri.
Men de unge, som med honom uppväxte voro, talade med honom, och sade: Så skall du säga till folket, som till dig talat hafver, och säger: Din fader hafver gjort vårt ok allt för tungt, gör du vårt ok lättare; och säg till dem: Mitt minsta finger skall vara tjockare än mins faders länder.
11 Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.’”
Hafver nu min fader för tungt ok lagt uppå eder, så skall jag ännu göra edart ok tyngre; min fader hafver tuktat eder med gisslar, men jag med scorpioner.
12 Bayan kwana uku sai Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam, yadda sarki ya ce, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
Som nu Jerobeam och allt folket kom till Rehabeam på tredje dagen, såsom Konungen sagt hade: Kommer igen till mig på tredje dagen;
13 Sarki ya amsa musu da kakkausar murya. Ya ƙi shawarar dattawan,
Svarade Konungen dem hårdeliga; och Konung Rehabeam öfvergaf de äldstas råd;
14 ya kuma bi shawarar matasan ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; zan ma sa mafi nauyi. Mahaifina ya bulale ku da bulala; zan bulale ku da kunamai.”
Och talade med dem efter de ungas råd, och sade: Hafver min fader gjort edart ok för svårt, så skall jag ännu göra det svårare; min fader hafver tuktat eder med gisslar, men jag med scorpioner.
15 Saboda haka sarki bai saurari mutane ba, gama wannan juyin al’amura daga Allah ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi ga Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya mutumin Shilo.
Alltså hörde Konungen folket intet; ty det vardt alltså vändt af Gudi, på det Herren skulle göra sitt ord fast, som han talat hade genom Ahia af Silo till Jerobeam, Nebats son.
16 Sa’ad da Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, suka ce, “Wanda rabo muke da shi a wurin Dawuda, wanda sashe muke da shi daga ɗan Yesse? Kowa yă koma tentinsa, ya Isra’ila! Ka lura da gidanka, ya Dawuda!” Saboda haka dukan Isra’ilawa suka tafi gida.
Då nu hele Israel såg, att Konungen intet hörde dem, svarade folket Konungenom, och sade: Hvad del hafve vi med David, eller arf med Isai son? Hvar och en af Israel drage till sina hyddor: Så se du nu till ditt hus, David. Och hele Israel gick i sina hyddor;
17 Amma game da Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da yin mulki a bisansu.
Så att Rehabeam regerade allenast öfver de Israels barn, som bodde i Juda städer.
18 Sarki Rehobowam ya aiki Hadoram wanda yake lura da aikin dole, amma Isra’ilawa suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sarki Rehobowam kuwa ya gaggauta ya shiga keken yaƙinsa ya gudu zuwa Urushalima.
Då sände Konung Rehabeam Hadoram räntomästaren; men Israels barn stenade honom ihjäl. Och Konung Rehabeam steg med hast på sin vagn, och flydde till Jerusalem.
19 Ta haka Isra’ila ya kasance cikin tawaye a kan gidan Dawuda har yă zuwa wannan rana.
Alltså föll Israel af ifrå Davids hus, allt intill denna dag.

< 2 Tarihi 10 >