< 2 Tarihi 1 >

1 Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
Salomon, fils de David, fut donc affermi dans la royauté, et le Seigneur son Dieu était avec lui; et le Seigneur l’éleva très haut.
2 Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
Et Salomon donna des ordres à tout Israël, aux tribuns, aux centurions, aux autres chefs, aux magistrats et aux princes des familles;
3 Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
Et il s’en alla avec toute la multitude au haut lieu de Gabaon, où était le tabernacle de l’alliance de Dieu, que fit Moïse, serviteur de Dieu, dans le désert.
4 Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
Quant à l’arche de Dieu, David l’avait amenée de Cariathiarim au lieu qu’il lui avait préparé, et où il lui avait dressé un tabernacle, c’est-à-dire à Jérusalem.
5 Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
Mais l’autel d’airain qu’avait fait Béséléel fils d’Uri, fils de Hur, était resté là devant le tabernacle du Seigneur; et Salomon alla le chercher, lui et toute l’assemblée.
6 Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
Et Salomon monta sur l’autel d’airain devant le tabernacle de l’alliance du Seigneur, et il y offrit mille hosties.
7 A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
Or voilà qu’en cette nuit même Dieu lui apparut, disant: Demande ce que tu veux que je te donne.
8 Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
Alors Salomon dit à Dieu: C’est vous qui avez fait une grande miséricorde à David, mon père, et qui m’avez établi roi à sa place.
9 To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
Maintenant donc, Seigneur Dieu, qu’elle s’accomplisse, la promesse que vous avez faite à David, mon père: car c’est vous qui m’avez établi roi sur votre peuple, qui est aussi innombrable que la poussière de la terre.
10 Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
Donnez-moi de la sagesse et de l’intelligence, enfin que j’entre et sorte devant votre peuple; car qui peut juger dignement ce peuple qui est vôtre, et qui est si grand?
11 Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
Alors Dieu répondit à Salomon: Parce que cela a plu de préférence à ton cœur, et que tu ne m’as point demandé des richesses, ni des biens, ni de la gloire, ni les âmes de ceux qui te haïssent, ni des jours de vie très nombreux; mais que tu as demandé de la sagesse et de la science, afin que tu puisses juger mon peuple sur lequel je t’ai établi roi:
12 saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
La sagesse et la science te sont données; et quant à des richesses, à des biens, à de la gloire, je t’en donnerai de telle sorte, que nul parmi les rois, ni avant toi, ni après toi, n’aura été semblable à toi.
13 Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
Salomon vint donc du haut lieu de Gabaon à Jérusalem, devant le tabernacle d’alliance, et il régna sur Israël.
14 Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
Et il rassembla des chars et des cavaliers; on lui disposa mille quatre cents chariots et douze mille cavaliers, et il les fit mettre dans les villes des quadriges, et près du roi à Jérusalem.
15 Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
Et le roi rendit l’or et l’argent communs comme les pierres dans Jérusalem, et les cèdres comme les sycomores qui croissent dans les plaines en grande quantité.
16 Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
Mais les chevaux lui étaient amenés d’Égypte et de Coa par les marchands du roi, qui y allaient et les achetaient,
17 Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.
Un attelage de quatre chevaux, six cents sicles d’argent, et un cheval, cent cinquante; et c’est ainsi que dans tous les royaumes des Héthéens, et par tous les rois de Syrie, la vente se pratiquait.

< 2 Tarihi 1 >