< 2 Tarihi 1 >
1 Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
And Solomon the son of David was strengthened in his kingdom, and the Lord his God was with him, and magnified him to a high degree.
2 Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
And Solomon gave orders to all Israel, to the captains of thousands, and of hundreds, and to the rulers, and to the judges of all Israel, and the heads of the families:
3 Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
And he went with all the multitude to the high place of Gabaon, where was the tabernacle of the covenant of the Lord, which Moses the servant of God made, in the wilderness.
4 Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
For David had brought the ark of God from Cariathiarim to the place, which he had prepared for it, and where he had pitched a tabernacle for it, that is, in Jerusalem.
5 Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
And the altar of brass, which Beseleel the son of Uri the son of Hur had made, was there before the tabernacle of the Lord: and Solomon and all the assembly sought it:
6 Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
And Solomon went up thither to the brazen altar, before the tabernacle of the covenant of the Lord, and offered up on it a thousand victims.
7 A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
And behold that night God appeared to him, saying: Ask what thou wilt that I should give thee.
8 Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
And Solomon said to God: Thou hast shewn great kindness to my father David: and hast made me king in his stead.
9 To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
Now therefore, O Lord God, let thy word be fulfilled, which thou hast promised to David my father: for thou hast made me king over thy great people, which is as innumerable as the dust of the earth.
10 Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
Give me wisdom and knowledge that I may come in and go out before thy people: for who can worthily judge this thy people, which is so great?
11 Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
And God said to Solomon: Because this choice hath pleased thy heart, and thou hast not asked riches, and wealth, and glory, nor the lives of them that hate thee, nor many days of life: but hast asked wisdom and knowledge, to be able to judge my people, over which I have made thee king,
12 saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
Wisdom and knowledge are granted to thee: and I will give thee riches, and wealth, and glory, so that none of the kings before thee, nor after thee, shall be like thee.
13 Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
Then Solomon came from the high place of Gabaon to Jerusalem before the tabernacle of the covenant, and reigned over Israel.
14 Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
And he gathered to himself chariots and horsemen, and he had a thousand four hundred chariots, and twelve thousand horsemen: and he placed them in the cities of the chariots, and with the king in Jerusalem.
15 Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
And the king made silver and gold to be in Jerusalem as stones, and cedar trees as sycamores, which grow in the plains in great multitude.
16 Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
And there were horses brought him from Egypt, and from Coa by the king’s merchants, who went, and bought at a price,
17 Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.
A chariot of four horses for six hundred pieces of silver, and a horse for a hundred and fifty: in like manner market was made in all the kingdoms of the Hethites, and of the kings of Syria.