< 1 Timoti 6 >
1 Duk waɗanda suke ƙarƙashin bauta, ya kamata su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci girmamawa matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwarmu.
Awa ehi niakole pihe nijoki anga atugwa ahoeele iakulu ao anga niakete ikulyo lehi, yeanonee itume uu nsoko elina lang'wi Tunda nuumanyisigwa uleke kulukilwa.
2 Waɗanda suke da iyayengiji masu bi, to, kada su yi musu reni domin su’yan’uwa ne. A maimako, sai ma su fi bauta musu, saboda waɗanda suke cin moriyar hidimarsu masu bi ne, ƙaunatattu ne kuma a gare su. Waɗannan su ne abubuwan da za ka koya musu ka kuma gargaɗe su.
Iatugwa niakete iakulu niahuie aleke kuamela kunsoko nianso aluna. Kuleke nianso manyisa nukutanantya imakani aya.
3 In wani yana koyarwar ƙarya bai kuma yarda da sahihiyar koyarwar Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma koyarwa ta tsoron Allah ba,
Ang'wi muntu fulani ukumanyisa kuuubi hange shuusingiye imalengaso itu aya nakuelekile, nae nkani nia mukulu u Yesu Kilisto, ang'wi shanga akugomba imanyiso niletongeela muuhueli.
4 yana cike da girman kai bai kuma san kome ba. Yana da mugun halin son gardama da muhawwara game da kalmomin da suke kawo kishi, rikici, maganar ƙeta, da mugayen zace-zace
Umuntu uyu ukikumbula hange shuine lehi. kuleka gwa, ukete ulei nuwikungumi munkani. Inkani izi yetuga welu, wilei, wisensi, usuki nuubi,
5 da yawan tankiya tsakanin mutane masu mugun hali, waɗanda aka raba su da gaskiya, suke kuma tsammani cewa bin Allah wata hanya ce ta samun kuɗi.
hange kiogo nikama tungotungo muantu imahala ao abepile. Amelekile itai. Asigile kina uuhueli nzila augole.
6 Amma bin Allah da gamsuwa riba ce mai yawa.
Itungeli uhueli nukugomba nsailo nkulu.
7 Gama ba mu zo duniya da kome ba, ba kuwa za mu fita daga cikinta da kome ba.
Kundogoilyo singaeukuzile nikentu munu mihe. Hange shakuohola kentu kehi kupuma munu mihe.
8 In dai muna da abinci da sutura, ai, sai mu gamsu da su.
Kuleka nianso, kukoneleke nindya niang'wenda.
9 Mutanen da suke son yin arziki sukan fāɗi cikin jarraba, su fāɗa a tarko, suna mugayen sha’awace-sha’awace iri-iri na wauta da cutarwa, irin waɗanda suke dulmuyar da mutane, su kai ga lalacewa da hallaka.
Itungeli awa niakulula akete insao igwiza mumagenywe, kukiila ukutegwa. Igwiza kuupungu nuedu ninsula mbi, hange mumaintu ehi neiatenda iantu apike muulimeli nuubi.
10 Gama son kuɗi shi ne tushen kowane irin mugun abu. Waɗansu mutane, don tsananin son kuɗi, sun bauɗe daga bangaskiya suka kuma jawo wa kansu da baƙin ciki iri-iri.
Kunsoko kulowa impia inge ng'wandyo nuakila uubi. Iantu niakete insula nanso, alimeigwe kule nuukueli hange isonsile ienso kuukia nuedu.
11 Amma kai, mutumin Allah, ka guji duk wannan, ka kuma nemi adalci, tsoron Allah, bangaskiya, ƙauna, jimrewa da kuma hankali.
Kuite uewe muntu nuang'wi Tunda, mamanke imakani nanso. Mityate ekulu, utaua, uhueli, ulowa, wigigimeeli, nuupolo.
12 Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios )
Ikue embita nenza nauhueli. Ambiela upanga nuakale nuilangiwe. Inge aensoko seye kina aupumilye uwihengi ntongeela aakueli udu kuiiki nekiza. (aiōnios )
13 Na umarce ka, a gaban Allah mai ba da rai ga kome, da kuma Kiristi Yesu wanda yayinda yake ba da shaida a gaban Buntus Bilatus ya yi kyakkyawar shaida,
Kuupa ilago ele ntongeela ang'wi Tunda nuezusokilye imaintu ehi ikie, hange ntongeela ang'wa Yesu Kilisto, nauligitilye itai kung'wa Pontio Pilato.
14 ka kiyaye wannan umarni ba tare da wani aibi ko abin zargi ba har yă bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi,
Kendegeela ilago kuutimeeli, wezewimugila kuaiilya, singa ukia kumukulu witu u Yesu Kilisto.
15 wanda Allah zai kawo a daidai lokaci, Allah, mai albarka wanda yake kaɗai Mai Mulki, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji,
Itunda ukigeelya uezi wakwe kumatungo yayo - Itunda, ukembetilwe, ngulu zizodu, Mtemi muamukulu, Mkulu nukuligilya.
16 wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios )
Ung'wenso du ukikie nikale hange nuikie muwelu nishawihugelwe. Kutile umuntu nuhumilekumuona hange nuhumile kumugoza. Kung'waakwe itule ikulyo nuuhumi nuakale. Huela. (aiōnios )
17 Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn )
Aile iagole niamunkumbigulu uwu alekekikumbula, hange aheje uuhueli muugole, nesinga watai. Kuleka nianso, yeanonee kue kumuhuela Itunda. Nuikupeza uugole wihi nuatai nsoko kulowe. (aiōn )
18 Ka umarce su su yi nagarta, su wadatu cikin ayyuka nagari, su kuma zama masu bayarwa hannu sake da kuma masu niyyar yin taimako.
Aile iatenda maza, agolipe mumilimo nimiza, atule akende, nukugomba kupumya.
19 Ta haka za su ajiye wa kansu dukiya a matsayin tushen mai ƙarfi don tsara mai zuwa, don su riƙi rai wanda yake na tabbatacce.
Kunzila eye akiekilya kitako nikiza kumakani nazile, nsoko kina ahume kuamba likalo ulyenso
20 Timoti, ka lura da abin da aka danƙa maka amana. Ka yi nesa da masu maganganun rashin tsoron Allah da kuma yawan mūsu da ake ƙarya, ake ce da shi ilimi,
Timoteo, kisunge iki nupegilwe iheje nuudui nuakipungu nuwikungumi nuakigilya nueze wauteele wiheja uhugu.
21 wanda waɗansu suka furta kuma ta yin haka suka bauɗe daga bangaskiya. Alheri yă kasance tare da ku.
Iantu ang'wi itanantya imakani aya, neite aulya uuhueli Uukende ulule ukole palung'wi nue.