< 1 Timoti 6 >

1 Duk waɗanda suke ƙarƙashin bauta, ya kamata su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci girmamawa matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwarmu.
Akik iga alatt vannak, mint szolgák, urukat teljes tiszteletre méltóknak tartsák, hogy miattuk Isten nevét és a tanítást ne káromolják.
2 Waɗanda suke da iyayengiji masu bi, to, kada su yi musu reni domin su’yan’uwa ne. A maimako, sai ma su fi bauta musu, saboda waɗanda suke cin moriyar hidimarsu masu bi ne, ƙaunatattu ne kuma a gare su. Waɗannan su ne abubuwan da za ka koya musu ka kuma gargaɗe su.
Akiknek pedig hívő uruk van, azokat ne becsüljék le, hanem annál inkább szolgáljanak nekik, hiszen atyafiak, hívők és szeretettek, akik jó cselekedetekben buzgólkodnak. Ezeket tanítsd és hirdesd!
3 In wani yana koyarwar ƙarya bai kuma yarda da sahihiyar koyarwar Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma koyarwa ta tsoron Allah ba,
Ha valaki másként tanít, és nem követi a mi Urunk Jézus Krisztus egészséges igéjét és az istenfélelem szerint való tanítást,
4 yana cike da girman kai bai kuma san kome ba. Yana da mugun halin son gardama da muhawwara game da kalmomin da suke kawo kishi, rikici, maganar ƙeta, da mugayen zace-zace
az felfuvalkodott, aki semmit sem ért, hanem vitatkozások és szóharcok betege, amiből csak irigység, viszálykodás, istenkáromlás, rosszindulatú gyanúsítás származik.
5 da yawan tankiya tsakanin mutane masu mugun hali, waɗanda aka raba su da gaskiya, suke kuma tsammani cewa bin Allah wata hanya ce ta samun kuɗi.
Megbomlott elméjű és az igazságtól megfosztott emberek hiábavaló torzsalkodása mindez, akik az istenfélelmet nyerészkedésnek tekintik.
6 Amma bin Allah da gamsuwa riba ce mai yawa.
De valóban nagy nyereség az istenfélelem megelégedéssel,
7 Gama ba mu zo duniya da kome ba, ba kuwa za mu fita daga cikinta da kome ba.
mert semmit sem hoztunk a világra, világos, hogy ki sem vihetünk semmit,
8 In dai muna da abinci da sutura, ai, sai mu gamsu da su.
de ha van élelmünk és ruházatunk, elégedjünk meg vele.
9 Mutanen da suke son yin arziki sukan fāɗi cikin jarraba, su fāɗa a tarko, suna mugayen sha’awace-sha’awace iri-iri na wauta da cutarwa, irin waɗanda suke dulmuyar da mutane, su kai ga lalacewa da hallaka.
Akik pedig meg akarnak gazdagodni, kísértésbe, csapdába és sok esztelen és káros kívánságba esnek, amelyek az embert veszedelembe és romlásba döntik.
10 Gama son kuɗi shi ne tushen kowane irin mugun abu. Waɗansu mutane, don tsananin son kuɗi, sun bauɗe daga bangaskiya suka kuma jawo wa kansu da baƙin ciki iri-iri.
Mert minden rossznak gyökere a pénz szerelme, amely után sóvárogva egyesek eltévelyednek a hittől, és sok fájdalmat okoznak önmaguknak.
11 Amma kai, mutumin Allah, ka guji duk wannan, ka kuma nemi adalci, tsoron Allah, bangaskiya, ƙauna, jimrewa da kuma hankali.
Te pedig, Isten embere, ezeket kerüld. Ellenben kövesd az igazságot, az istenfélelmet, a hitet, a szeretetet, a békességes tűrést, a szelídséget.
12 Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios g166)
Harcold meg a hitnek szép harcát, nyerd el az örök életet, amelyre elhívattál, és amelyről vallást tettél szép hitvallással sok tanú előtt. (aiōnios g166)
13 Na umarce ka, a gaban Allah mai ba da rai ga kome, da kuma Kiristi Yesu wanda yayinda yake ba da shaida a gaban Buntus Bilatus ya yi kyakkyawar shaida,
Meghagyom neked Isten színe előtt, aki életet ad mindennek, és Krisztus Jézus előtt, aki bizonyságot tett Poncius Pilátus előtt azzal a szép hitvallással,
14 ka kiyaye wannan umarni ba tare da wani aibi ko abin zargi ba har yă bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi,
hogy tartsd meg a parancsolatot mocsoktalanul, feddhetetlenül a mi Urunk Jézus Krisztus megjelenéséig,
15 wanda Allah zai kawo a daidai lokaci, Allah, mai albarka wanda yake kaɗai Mai Mulki, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji,
amelyet a maga idejében megmutat a boldog és egyedül hatalmas, a királyok királya és az uraknak Ura.
16 wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios g166)
Egyedül övé a halhatatlanság, aki hozzáférhetetlen világosságban lakik, akit az emberek közül senki sem látott, nem is láthat, akinek tisztesség és örökkévaló hatalom! Ámen. (aiōnios g166)
17 Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn g165)
Azoknak pedig, akik gazdagok e világon, mondd meg, hogy ne fuvalkodjanak fel, és ne reménykedjenek a bizonytalan gazdagságban, hanem az élő Istenben, aki bőségesen megad nekünk mindent megélhetésünkre. (aiōn g165)
18 Ka umarce su su yi nagarta, su wadatu cikin ayyuka nagari, su kuma zama masu bayarwa hannu sake da kuma masu niyyar yin taimako.
Tegyenek jót, legyenek gazdagok a jó cselekedetekben, szívesen adakozzanak, és osszák meg javaikat másokkal,
19 Ta haka za su ajiye wa kansu dukiya a matsayin tushen mai ƙarfi don tsara mai zuwa, don su riƙi rai wanda yake na tabbatacce.
és így a jövőt megalapozó kincset gyűjtsenek, hogy elnyerjék az örök életet.
20 Timoti, ka lura da abin da aka danƙa maka amana. Ka yi nesa da masu maganganun rashin tsoron Allah da kuma yawan mūsu da ake ƙarya, ake ce da shi ilimi,
Timóteus, őrizd meg, ami rád van bízva. Fordulj el a szentségtelen, üres beszédektől és a hamis tanítás ellenvetéseitől,
21 wanda waɗansu suka furta kuma ta yin haka suka bauɗe daga bangaskiya. Alheri yă kasance tare da ku.
amelyet egyesek hirdetnek, és a hittől eltévelyedtek. Kegyelem legyen veled! Ámen.

< 1 Timoti 6 >