< 1 Timoti 6 >
1 Duk waɗanda suke ƙarƙashin bauta, ya kamata su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci girmamawa matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwarmu.
All who are under the yoke of slavery must regard their own masters as worthy of all honor, so that no one will revile God's name or his doctrine.
2 Waɗanda suke da iyayengiji masu bi, to, kada su yi musu reni domin su’yan’uwa ne. A maimako, sai ma su fi bauta musu, saboda waɗanda suke cin moriyar hidimarsu masu bi ne, ƙaunatattu ne kuma a gare su. Waɗannan su ne abubuwan da za ka koya musu ka kuma gargaɗe su.
Slaves who have believing masters must not despise them, for they are brothers; rather they must serve them, because those who benefit from their good service are faithful and beloved. Teach and encourage these things.
3 In wani yana koyarwar ƙarya bai kuma yarda da sahihiyar koyarwar Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma koyarwa ta tsoron Allah ba,
If anyone teaches a different doctrine and does not agree with the sound words of our Lord Jesus Christ and the teaching that is in accordance with godliness,
4 yana cike da girman kai bai kuma san kome ba. Yana da mugun halin son gardama da muhawwara game da kalmomin da suke kawo kishi, rikici, maganar ƙeta, da mugayen zace-zace
he is puffed up and understands nothing. Moreover, he has an unhealthy desire for controversies and quarrels about words, from which come envy, strife, slanderous words, evil suspicions,
5 da yawan tankiya tsakanin mutane masu mugun hali, waɗanda aka raba su da gaskiya, suke kuma tsammani cewa bin Allah wata hanya ce ta samun kuɗi.
and constant disagreement among people who are depraved in mind and deprived of the truth, supposing that godliness is a means of gain. Keep away from such people.
6 Amma bin Allah da gamsuwa riba ce mai yawa.
But godliness with contentment is great gain.
7 Gama ba mu zo duniya da kome ba, ba kuwa za mu fita daga cikinta da kome ba.
For we brought nothing into the world, and it is clear that we cannot bring anything out either,
8 In dai muna da abinci da sutura, ai, sai mu gamsu da su.
but if we have food and clothing, we will be content with that.
9 Mutanen da suke son yin arziki sukan fāɗi cikin jarraba, su fāɗa a tarko, suna mugayen sha’awace-sha’awace iri-iri na wauta da cutarwa, irin waɗanda suke dulmuyar da mutane, su kai ga lalacewa da hallaka.
But those who wish to be rich fall into temptation and a snare, and into many senseless and harmful desires that sink people into ruin and destruction.
10 Gama son kuɗi shi ne tushen kowane irin mugun abu. Waɗansu mutane, don tsananin son kuɗi, sun bauɗe daga bangaskiya suka kuma jawo wa kansu da baƙin ciki iri-iri.
For the love of money is the root of all kinds of evil, and in their eagerness to become rich some have wandered away from the faith, piercing themselves with many sorrows.
11 Amma kai, mutumin Allah, ka guji duk wannan, ka kuma nemi adalci, tsoron Allah, bangaskiya, ƙauna, jimrewa da kuma hankali.
But as for yoʋ, O man of God, flee from these things, and pursue righteousness, godliness, faithfulness, love, endurance, and gentleness.
12 Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios )
Fight the good fight of faith. Take hold of the eternal life to which yoʋ were called and concerning which yoʋ made the good confession in the presence of many witnesses. (aiōnios )
13 Na umarce ka, a gaban Allah mai ba da rai ga kome, da kuma Kiristi Yesu wanda yayinda yake ba da shaida a gaban Buntus Bilatus ya yi kyakkyawar shaida,
I charge yoʋ before God, who gives life to all things, and before Christ Jesus, who made the good confession in his testimony before Pontius Pilate,
14 ka kiyaye wannan umarni ba tare da wani aibi ko abin zargi ba har yă bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi,
that yoʋ obey what has been commanded without fault or reproach until the appearing of our Lord Jesus Christ,
15 wanda Allah zai kawo a daidai lokaci, Allah, mai albarka wanda yake kaɗai Mai Mulki, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji,
which God will reveal in his own time. He is the blessed and only Sovereign, the King of kings and Lord of lords,
16 wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios )
who alone has immortality, dwelling in unapproachable light, whom no man has ever seen or is able to see. To him be honor and eternal power. Amen. (aiōnios )
17 Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn )
Command those who are rich in this present age not to be haughty or to put their hope in the uncertainty of riches, but in the living God, who richly provides us with everything for our enjoyment. (aiōn )
18 Ka umarce su su yi nagarta, su wadatu cikin ayyuka nagari, su kuma zama masu bayarwa hannu sake da kuma masu niyyar yin taimako.
Command them to do good, to be rich in good works, and to be generous and willing to share,
19 Ta haka za su ajiye wa kansu dukiya a matsayin tushen mai ƙarfi don tsara mai zuwa, don su riƙi rai wanda yake na tabbatacce.
treasuring up for themselves a good foundation for the time to come, so that they may take hold of eternal life.
20 Timoti, ka lura da abin da aka danƙa maka amana. Ka yi nesa da masu maganganun rashin tsoron Allah da kuma yawan mūsu da ake ƙarya, ake ce da shi ilimi,
O Timothy, guard what has been entrusted to yoʋ and avoid the profane chatter and counterarguments of what is falsely called “knowledge.”
21 wanda waɗansu suka furta kuma ta yin haka suka bauɗe daga bangaskiya. Alheri yă kasance tare da ku.
By professing it, some have strayed from the faith. Grace be with yoʋ. Amen.