< 1 Timoti 2 >
1 Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
J’exhorte donc, avant toutes choses, à faire des supplications, des prières, des intercessions, des actions de grâces pour tous les hommes,
2 da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
– pour les rois et pour tous ceux qui sont haut placés, afin que nous puissions mener une vie paisible et tranquille, en toute piété et honnêteté;
3 Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
car cela est bon et agréable devant notre Dieu sauveur,
4 wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
qui veut que tous les hommes soient sauvés et viennent à la connaissance de la vérité;
5 Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
car Dieu est un, et le médiateur entre Dieu et les hommes est un, [l’]homme Christ Jésus,
6 wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
qui s’est donné lui-même en rançon pour tous, témoignage [qui devait être rendu] en son propre temps,
7 Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
pour lequel moi, j’ai été établi prédicateur et apôtre (je dis la vérité, je ne mens pas), docteur des nations dans la foi et dans la vérité.
8 Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
Je veux donc que les hommes prient en tout lieu, élevant des mains saintes, sans colère et sans raisonnement.
9 Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
De même aussi, que les femmes se parent d’un costume décent, avec pudeur et modestie, non pas de tresses et d’or, ou de perles, ou d’habillements somptueux,
10 sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
mais par de bonnes œuvres, ce qui sied à des femmes qui font profession de servir Dieu.
11 Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
Que la femme apprenne dans le silence, en toute soumission;
12 Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
mais je ne permets pas à la femme d’enseigner ni d’user d’autorité sur l’homme; mais elle doit demeurer dans le silence;
13 Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
car Adam a été formé le premier, et puis Ève;
14 Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
et Adam n’a pas été trompé; mais la femme, ayant été trompée, est tombée dans la transgression;
15 Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.
mais elle sera sauvée en enfantant, si elles persévèrent dans la foi et l’amour et la sainteté, avec modestie.