< 1 Timoti 2 >

1 Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
This then I exhort thee first of all, that supplications, prayers, intercessions, and thanksgivings he made for all men;
2 da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
particularly for kings, and all that are in authority, that we may lead a quiet and peaceful life in all piety and virtue.
3 Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
For this is good and acceptable in the sight of God our Saviour:
4 wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
who is willing that all men should be saved, and therefore come to the knowledge of the truth.
5 Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
For there is one God, and one Mediator between God and men, the man Christ Jesus:
6 wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
who gave himself a ransom for all, a testimony to be published in due time,
7 Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
for which I was appointed a herald and an apostle. I speak the truth in Christ, I lie not; I am a teacher of the Gentiles in faith and truth.
8 Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
I direct therefore that men pray in every place, lifting up holy hands without wrath and debate:
9 Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
likewise that women dress themselves in decent apparel with modesty and prudence, not in braided hair, or gold, or pearls, or costly garments;
10 sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
but in good works, as becometh women professing godliness.
11 Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
Let the woman learn in silence with all submission: but I permit not a woman to teach,
12 Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
nor to usurp authority over the man, but to be silent.
13 Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
For Adam was formed first, then Eve.
14 Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
And Adam was not seduced by the serpent, but the woman being led astray was first in the transgression.
15 Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.
Yet shall she be saved through childbirth, if they continue in faith and love, in holiness and modesty.

< 1 Timoti 2 >