< 1 Timoti 2 >
1 Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
Now I exhort, first of all, that supplications, prayers, intercessions, and thanksgivings be made for all men;
2 da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
for kings, and all who are in authority, that we may lead a quiet and peaceable life in all godliness and honesty.
3 Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
For this is good and acceptable in the sight of God our Saviour,
4 wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
who wills all men to be saved, and to come to an acknowledgment of the truth.
5 Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
For there is one God, and one mediator between God and men, --the man Christ Jesus,
6 wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
who gave himself a ransom for all; --of which the testimony is in its proper season:
7 Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
for which I was appointed a herald and an Apostle, (I speak the truth, I do not falsify, ) a teacher to the Gentiles in faith and truth.
8 Ina so maza a ko’ina su ɗaga hannuwansu masu tsarki cikin addu’a, ba tare da fushi ko faɗa ba.
I will, therefore, that the men pray everywhere, lifting up holy hands, without wrath and disputings.
9 Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
I like manner also, that the women adorn themselves in decent apparel, with modesty and sobriety, not with plaited hair, or gold, or pearls, or costly raiment:
10 sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
but (which becomes women professing godliness, ) with good works.
11 Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
Let a woman learn in silence with all submission:
12 Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
for I do not allow a woman to teach, nor to usurp authority over a man, but to be silent;
13 Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
for Adam was first formed, then Eve.
14 Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
Besides, Adam was not deceived: but the woman, being deceived, was in transgression.
15 Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.
However, she shall be saved through child-bearing, if they live in faith, and love, and holiness, with sobriety.