< 1 Tessalonikawa 5 >

1 To,’yan’uwa, game da lokuta da ranaku, ba ma bukata mu rubuta muku,
Über Zeit und Zeitumstände, Brüder, ist nicht Not, euch zu schreiben;
2 gama kun sani sarai cewa ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo da dare.
Ihr wißt ja selbst genau, daß der Tag des Herrn kommen wird wie ein Dieb in der Nacht.
3 Yayinda mutane suke cewa, “Akwai salama da zaman lafiya,” hallaka za tă auko musu farat ɗaya, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba za su kuwa tsira ba.
Denn wenn sie sagen: Es ist Friede, ist keine Gefahr, so steht plötzlich das Verderben vor der Tür, wie die Wehen vor dem Weib, das gebären soll; und sie können nicht entfliehen.
4 Amma ku,’yan’uwa, ba kwa cikin duhu da wannan rana za tă zo muku ba zato kamar ɓarawo.
Ihr aber, Brüder, seid nicht in Finsternis, so daß euch der Tag wie der Dieb überfalle.
5 Dukanku’ya’yan haske ne da kuma’ya’yan rana. Mu ba mutanen dare ko na duhu ba ne.
Ihr alle seid ja Kinder des Lichts und Kinder des Tags; wir sind nicht von der Nacht, noch von der Finsternis.
6 Saboda haka fa, kada mu zama kamar saura, waɗanda suke barci, sai dai mu zama masu tsaro da masu kamunkai.
So laßt uns denn nicht schlafen, wie die anderen, sondern wachen und nüchtern sein.
7 Gama masu barci, da dad dare suke barci, masu sha su bugu kuwa, da dad dare suke buguwa.
Denn die da schlafen, schlafen in der Nacht, und die da trunken sind, sind trunken in der Nacht.
8 Amma da yake mu na rana ne, bari mu zama masu kamunkai, sanye da bangaskiya da ƙauna kamar sulke, begen cetonmu kuma kamar hular kwano.
Wir aber, die wir vom Tage sind, wollen nüchtern sein, mit dem Panzer des Glaubens und der Liebe angetan, und mit dem Helm der Hoffnung zur Seligkeit.
9 Gama Allah bai naɗa mu don mu sha fushi ba, sai dai mu sami ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Denn Gott hat uns nicht gesetzt zum Zorn, sondern zur Erlangung der Seligkeit durch unseren Herrn Jesus Christus, Der für uns gestorben ist.
10 Ya mutu saboda mu domin, ko muna a faɗake ko muna barci, mu kasance tare da shi.
Auf daß wir, ob wir wachen oder schlafen, zugleich mit Ihm leben sollen.
11 Saboda haka ku ƙarfafa juna ku kuma gina juna, kamar dai yadda kuke yi.
Darum ermahnt einander und erbaue einer den anderen, wie ihr denn auch tut.
12 To, muna roƙonku,’yan’uwa, ku girmama waɗanda suke aiki sosai a cikinku, waɗanda suke bisanku cikin Ubangiji da kuma waɗanda suke yin muku gargaɗi.
Wir bitten euch aber, Brüder, daß ihr sorgt für die, welche an euch arbeiten und euch vorstehen in dem Herrn und euch vermahnen.
13 Ku riƙe su da mutunci sosai cikin ƙauna saboda aikinsu. Ku yi zaman lafiya da juna.
Und haltet sie hoch in eurer Liebe, um ihres Werkes willen. Haltet Frieden untereinander.
14 Muna kuma gargaɗe ku,’yan’uwa, ku gargaɗe waɗanda suke zaman banza, ku ƙarfafa masu raunanar zuciya, ku taimaki marasa ƙarfi, ku yi haƙuri da kowa.
Wir ermahnen euch aber, liebe Brüder, weiset zurecht die Unordentlichen, tröstet die Kleinmütigen, nehmt euch der Schwachen an, seid langmütig gegen alle.
15 Ku tabbata cewa kada kowa yă rama mugunta da mugunta, sai dai kullum ku yi ƙoƙarin yin wa juna alheri da kuma dukan mutane.
Seht darauf, daß keiner Böses mit Bösem vergelte, sondern jagt allezeit dem Guten nach, beides, untereinander und gegen jedermann.
16 Ku riƙa farin ciki kullum;
Seid allezeit frohen Mutes.
17 ku ci gaba da yin addu’a;
Betet ohne Unterlaß.
18 ku yi godiya cikin kowane hali, gama wannan shi ne nufin Allah dominku cikin Kiristi Yesu.
Seid dankbar in allen Dingen, denn das ist der Wille Gottes in Christus Jesus an euch.
19 Kada ku danne aikin Ruhu.
Den Geist dämpfet nicht.
20 Kada ku rena annabci,
Mißachtet nicht Weissagungen,
21 amma ku gwada kome, ku riƙe abin da yake mai kyau,
Sondern prüft alles, das Gute behaltet!
22 ku ƙi kowace mugunta.
Meidet allen bösen Schein.
23 Bari Allah da kansa, Allah na salama, yă tsarkake ku sarai. Bari dukan ruhunku, ranku, da kuma jikinku su zama marar aibi a dawowar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Er aber, der Gott des Friedens, heilige euch durch und durch, und Geist, Seele und Leib möge an euch völlig unsträflich erhalten werden für die Zukunft unseres Herrn Jesus Christus.
24 Wannan wanda ya kira ku mai aminci ne zai kuwa aikata.
Treu ist Er, Der euch ruft, und wird es auch vollbringen.
25 ’Yan’uwa, ku yi mana addu’a.
Brüder, betet für uns!
26 Ku gaggai da dukan’yan’uwa da sumba mai tsarki.
Grüßet alle Brüder mit dem heiligen Kuß.
27 Na gama ku da Ubangiji ku sa a karanta wannan wasiƙa ga dukan’yan’uwa.
Ich beschwöre euch bei dem Herrn, daß ihr diesen Brief alle heiligen Brüder lesen lasset.
28 Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku.
Die Gnade unseres Herrn Jesu Christi sei mit euch! Amen.

< 1 Tessalonikawa 5 >