< 1 Tessalonikawa 5 >

1 To,’yan’uwa, game da lokuta da ranaku, ba ma bukata mu rubuta muku,
But of the times and moments, brethren, you need not, that we should write to you;
2 gama kun sani sarai cewa ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo da dare.
For yourselves know perfectly, that the day of the Lord shall so come, as a thief in the night.
3 Yayinda mutane suke cewa, “Akwai salama da zaman lafiya,” hallaka za tă auko musu farat ɗaya, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba za su kuwa tsira ba.
For when they shall say, peace and security; then shall sudden destruction come upon them, as the pains upon her that is with child, and they shall not escape.
4 Amma ku,’yan’uwa, ba kwa cikin duhu da wannan rana za tă zo muku ba zato kamar ɓarawo.
But you, brethren, are not in darkness, that that day should overtake you as a thief.
5 Dukanku’ya’yan haske ne da kuma’ya’yan rana. Mu ba mutanen dare ko na duhu ba ne.
For all you are the children of light, and children of the day: we are not of the night, nor of darkness.
6 Saboda haka fa, kada mu zama kamar saura, waɗanda suke barci, sai dai mu zama masu tsaro da masu kamunkai.
Therefore, let us not sleep, as others do; but let us watch, and be sober.
7 Gama masu barci, da dad dare suke barci, masu sha su bugu kuwa, da dad dare suke buguwa.
For they that sleep, sleep in the night; and they that are drunk, are drunk in the night.
8 Amma da yake mu na rana ne, bari mu zama masu kamunkai, sanye da bangaskiya da ƙauna kamar sulke, begen cetonmu kuma kamar hular kwano.
But let us, who are of the day, be sober, having on the breastplate of faith and charity, and for a helmet the hope of salvation.
9 Gama Allah bai naɗa mu don mu sha fushi ba, sai dai mu sami ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
For God hath not appointed us unto wrath, but unto the purchasing of salvation by our Lord Jesus Christ,
10 Ya mutu saboda mu domin, ko muna a faɗake ko muna barci, mu kasance tare da shi.
Who died for us; that, whether we watch or sleep, we may live together with him.
11 Saboda haka ku ƙarfafa juna ku kuma gina juna, kamar dai yadda kuke yi.
For which cause comfort one another; and edify one another, as you also do.
12 To, muna roƙonku,’yan’uwa, ku girmama waɗanda suke aiki sosai a cikinku, waɗanda suke bisanku cikin Ubangiji da kuma waɗanda suke yin muku gargaɗi.
And we beseech you, brethren, to know them who labour among you, and are over you in the Lord, and admonish you:
13 Ku riƙe su da mutunci sosai cikin ƙauna saboda aikinsu. Ku yi zaman lafiya da juna.
That you esteem them more abundantly in charity, for their work’s sake. Have peace with them.
14 Muna kuma gargaɗe ku,’yan’uwa, ku gargaɗe waɗanda suke zaman banza, ku ƙarfafa masu raunanar zuciya, ku taimaki marasa ƙarfi, ku yi haƙuri da kowa.
And we beseech you, brethren, rebuke the unquiet, comfort the feeble minded, support the weak, be patient towards all men.
15 Ku tabbata cewa kada kowa yă rama mugunta da mugunta, sai dai kullum ku yi ƙoƙarin yin wa juna alheri da kuma dukan mutane.
See that none render evil for evil to any man; but ever follow that which is good towards each other, and towards all men.
16 Ku riƙa farin ciki kullum;
Always rejoice.
17 ku ci gaba da yin addu’a;
Pray without ceasing.
18 ku yi godiya cikin kowane hali, gama wannan shi ne nufin Allah dominku cikin Kiristi Yesu.
In all things give thanks; for this is the will of God in Christ Jesus concerning you all.
19 Kada ku danne aikin Ruhu.
Extinguish not the spirit.
20 Kada ku rena annabci,
Despise not prophecies.
21 amma ku gwada kome, ku riƙe abin da yake mai kyau,
But prove all things; hold fast that which is good.
22 ku ƙi kowace mugunta.
From all appearance of evil refrain yourselves.
23 Bari Allah da kansa, Allah na salama, yă tsarkake ku sarai. Bari dukan ruhunku, ranku, da kuma jikinku su zama marar aibi a dawowar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
And may the God of peace himself sanctify you in all things; that your whole spirit, and soul, and body, may be preserved blameless in the coming of our Lord Jesus Christ.
24 Wannan wanda ya kira ku mai aminci ne zai kuwa aikata.
He is faithful who hath called you, who also will do it.
25 ’Yan’uwa, ku yi mana addu’a.
Brethren, pray for us.
26 Ku gaggai da dukan’yan’uwa da sumba mai tsarki.
Salute all the brethren with a holy kiss.
27 Na gama ku da Ubangiji ku sa a karanta wannan wasiƙa ga dukan’yan’uwa.
I charge you by the Lord, that this epistle be read to all the holy brethren.
28 Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku.
The grace of our Lord Jesus Christ be with you. Amen.

< 1 Tessalonikawa 5 >