< 1 Tessalonikawa 5 >
1 To,’yan’uwa, game da lokuta da ranaku, ba ma bukata mu rubuta muku,
Now about the times and seasons, brothers, we do not need to write to you.
2 gama kun sani sarai cewa ranar Ubangiji za tă zo kamar ɓarawo da dare.
For you are fully aware that the Day of the Lord will come like a thief in the night.
3 Yayinda mutane suke cewa, “Akwai salama da zaman lafiya,” hallaka za tă auko musu farat ɗaya, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba za su kuwa tsira ba.
While people are saying, “Peace and security,” destruction will come upon them suddenly, like labor pains on a pregnant woman, and they will not escape.
4 Amma ku,’yan’uwa, ba kwa cikin duhu da wannan rana za tă zo muku ba zato kamar ɓarawo.
But you, brothers, are not in the darkness so that this day should overtake you like a thief.
5 Dukanku’ya’yan haske ne da kuma’ya’yan rana. Mu ba mutanen dare ko na duhu ba ne.
For you are all sons of the light and sons of the day; we do not belong to the night or to the darkness.
6 Saboda haka fa, kada mu zama kamar saura, waɗanda suke barci, sai dai mu zama masu tsaro da masu kamunkai.
So then, let us not sleep as the others do, but let us remain awake and sober.
7 Gama masu barci, da dad dare suke barci, masu sha su bugu kuwa, da dad dare suke buguwa.
For those who sleep, sleep at night; and those who get drunk, get drunk at night.
8 Amma da yake mu na rana ne, bari mu zama masu kamunkai, sanye da bangaskiya da ƙauna kamar sulke, begen cetonmu kuma kamar hular kwano.
But since we belong to the day, let us be sober, putting on the breastplate of faith and love, and the helmet of our hope of salvation.
9 Gama Allah bai naɗa mu don mu sha fushi ba, sai dai mu sami ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
For God has not appointed us to suffer wrath, but to obtain salvation through our Lord Jesus Christ.
10 Ya mutu saboda mu domin, ko muna a faɗake ko muna barci, mu kasance tare da shi.
He died for us so that, whether we are awake or asleep, we may live together with Him.
11 Saboda haka ku ƙarfafa juna ku kuma gina juna, kamar dai yadda kuke yi.
Therefore encourage and build one another up, just as you are already doing.
12 To, muna roƙonku,’yan’uwa, ku girmama waɗanda suke aiki sosai a cikinku, waɗanda suke bisanku cikin Ubangiji da kuma waɗanda suke yin muku gargaɗi.
But we ask you, brothers, to acknowledge those who work diligently among you, who preside over you in the Lord and give you instruction.
13 Ku riƙe su da mutunci sosai cikin ƙauna saboda aikinsu. Ku yi zaman lafiya da juna.
In love, hold them in highest regard because of their work. Live in peace with one another.
14 Muna kuma gargaɗe ku,’yan’uwa, ku gargaɗe waɗanda suke zaman banza, ku ƙarfafa masu raunanar zuciya, ku taimaki marasa ƙarfi, ku yi haƙuri da kowa.
And we urge you, brothers, to admonish the unruly, encourage the fainthearted, help the weak, and be patient with everyone.
15 Ku tabbata cewa kada kowa yă rama mugunta da mugunta, sai dai kullum ku yi ƙoƙarin yin wa juna alheri da kuma dukan mutane.
Make sure that no one repays evil for evil. Always pursue what is good for one another and for all people.
16 Ku riƙa farin ciki kullum;
Rejoice at all times.
17 ku ci gaba da yin addu’a;
Pray without ceasing.
18 ku yi godiya cikin kowane hali, gama wannan shi ne nufin Allah dominku cikin Kiristi Yesu.
Give thanks in every circumstance, for this is God’s will for you in Christ Jesus.
19 Kada ku danne aikin Ruhu.
Do not extinguish the Spirit.
Do not treat prophecies with contempt,
21 amma ku gwada kome, ku riƙe abin da yake mai kyau,
but test all things. Hold fast to what is good.
Abstain from every form of evil.
23 Bari Allah da kansa, Allah na salama, yă tsarkake ku sarai. Bari dukan ruhunku, ranku, da kuma jikinku su zama marar aibi a dawowar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Now may the God of peace Himself sanctify you completely, and may your entire spirit, soul, and body be kept blameless at the coming of our Lord Jesus Christ.
24 Wannan wanda ya kira ku mai aminci ne zai kuwa aikata.
The One who calls you is faithful, and He will do it.
25 ’Yan’uwa, ku yi mana addu’a.
Brothers, pray for us as well.
26 Ku gaggai da dukan’yan’uwa da sumba mai tsarki.
Greet all the brothers with a holy kiss.
27 Na gama ku da Ubangiji ku sa a karanta wannan wasiƙa ga dukan’yan’uwa.
I charge you before the Lord to have this letter read to all the brothers.
28 Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ku.
The grace of our Lord Jesus Christ be with you.