< 1 Tessalonikawa 4 >
1 A ƙarshe,’yan’uwa, mun umarce ku yadda za ku yi rayuwa domin ku gamshi Allah, kamar yadda kuke yi. Yanzu muna roƙonku muna kuma gargaɗe ku a cikin Ubangiji Yesu ku yi haka sau da sau.
Hatimaye ndongo, tukabhapela n'teema ni kubhasiikwa Yesu Kristu. Kama kampokili maelekezo kuhomela kwa tete namna yai pasibhwa kulota na niyakampendesya K'yara, kwa njela eye kabh'ele mulotai ni kubhomba zaidi.
2 Gama kun san umarnan da muka ba ku ta wurin ikon Ubangiji Yesu.
Kwa ndabha mmanyili malobhi gani yatubhapelili kup'etela Bwana Yesu.
3 Nufin Allah ne a tsarkake ku, cewa ku guje wa fasikanci;
Kwa ndabha agha ndo mapenzi gha K'yara: utakasobhuinu- ndabha muyepukai zinaa,
4 don kowannenku yă koya yadda zai ƙame kansa a hanyar da take mai tsarki, mai mutunci kuma,
Ndabha Kila mmonga bhinu amanyili namna ya kumiliki n'dala munu muene ki utakatifu na kiheshima.
5 ba cikin muguwar sha’awa kamar ta marasa bangaskiya, waɗanda ba su san Allah ba;
Kotokuya ni n'dala kwajia tamaasa mumbhele (Kujo mataifa ghaghammanyili lepi K'yara).
6 cikin wannan al’amari kuwa kada wani yă yi wa ɗan’uwansa laifi ko yă cuce shi. Ubangiji zai hukunta mutane saboda dukan irin waɗannan zunubai, kamar yadda muka riga muka gaya muku, muka kuma yi muku gargaɗi.
Akotokuya munu yuoa yhola yaivukai mipaka kun'kosela ndongo munu kwajia ya lijambo ele. Kwa ndabha Bwana muene ndo yailepa kisasi kya mambo ghoa agha, kama katulongolili kubhaonya na kubhashuhudila.
7 Gama Allah bai kira mu ga zaman marasa tsarki ba, sai dai ga zaman tsarki.
Kwa ndabha Bwana atukutili lepi kwa uchafu, bali kitakatifu.
8 Saboda haka, duk wanda ya ƙi wannan umarni ba mutum ne ya ƙi ba sai ko Allah, wanda ya ba ku Ruhunsa Mai Tsarki.
Kwa eyu yakaibela ele yabhibela lepi bhanu, Bali akambela K'yara, yaakabhapela Roho N'takatifu bhuake.
9 Yanzu kuwa game da ƙaunar’yan’uwa, ba ma bukata mu rubuta muku, gama ku kanku Allah ya riga ya koya muku ku ƙaunaci juna.
Kuhusu upendo wa ndongo, iyelepi haja ya munu yuoa yhola kukuyandikila, kwa ndabha mfundisi bhu ni kyala kuganana yhomo kwa yhomo.
10 Gaskiyar kuwa ita ce, kuna ƙaunar dukan’yan’uwa ko’ina a Makidoniya. Duk da haka muna ƙara gargaɗe ku,’yan’uwa, ku yi haka sau da sau.
Hakika, mwaketili agha ghoa kwa bhalongo bhabhayele Makedonia iyoa, lakini tukabhasii, ndhongo, niketai hatani kuzidi.
11 Ku mai da wannan burinku na yi natsattsiyar rayuwa, kuna mai da hankali ga sha’anin da yake gabanku, kuna kuma yin aiki da hannuwanku, kamar dai yadda muka gaya muku,
Tu kabhasii mtamawiayi kuishi maisha gha kutulila, kujali mbhombho sinu, ni kufuanya mbhombho kwa mabhoko gha yhomo, kama katubhaamuili.
12 don rayuwanku ta kullum ta zama da mutunci ga waɗanda suke na waje don kuma kada ku dogara a kan kowa.
Fwanyai agha ili mubhwesi ayi kutola kinofu na kiheshima kwa abha bhabha yele kwibhala ni imani, ili usiponghokibhu ni lihitaji liyoalela.
13 ’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege.
Tilondelepi muenga muyetewai kayilondeka lepi, emu bhalongo, panani ya abha bhabha ghonili, ili msihidi kuhuzunika kwa bhamana bhabhayele lepi ni uhakika wa magono ghaghihida.
14 Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu.
Ikayelai lianimi kuwa Yesu afuili ni kifufuka kabh'ele, hata kabh'ele K'yara akabhaleta pamonga ni Yesu abha bhabhagonili kimauti kup'etela muene.
15 Bisa ga maganar Ubangiji kansa, muna gaya muku cewa mu da muke raye har yanzu, waɗanda aka bari har dawowar Ubangiji, tabbatacce ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba.
Kwajia ya agha. Tukabhajobhela muenga kwa lilobhi la Bwana, ndabha tete ya tuyele hai, yatuyelai magono gha kuhida muene Bwana, hakika tukabhalongolela bhala bhabhagonili kimauti.
16 Gama Ubangiji kansa zai sauko daga sama, da umarni mai ƙarfi, da muryar babban mala’ika da kuma busar ƙahon Allah, waɗanda suka mutu kuwa cikin Kiristi za su tashi da farko.
Kwa ndabha muene Bwana alaselela kuhomela kumabhengu. Alahida ni sauti ibhaa, pamonga ni sauti ya malaika bhakuu, pamonga ni palapanda ya K'yara, nabho bhabhafuili ku'etela Kristu bhalafufuka hosi.
17 Bayan haka, mu da muke da rai da aka bari, za a ɗauke mu tare da su a cikin gizagizai don mu sadu da Ubangiji a sararin sama. Ta haka za mu kasance tare da Ubangiji har abada.
Kabh'ele tete yatuyele hai yatubakili, tulaungana mmabhengu pamonga nabhu kumlaki Bwana muhewani. Kwa njela eye tulaya ni Bwana magono ghoa.
18 Saboda haka ku ƙarfafa juna da waɗannan kalmomi.
Kwa iyo, nyifalijiayi yhomo kwa yhomo kwa malobhi agha.