< 1 Tessalonikawa 4 >

1 A ƙarshe,’yan’uwa, mun umarce ku yadda za ku yi rayuwa domin ku gamshi Allah, kamar yadda kuke yi. Yanzu muna roƙonku muna kuma gargaɗe ku a cikin Ubangiji Yesu ku yi haka sau da sau.
For the rest therefore, brethren, we pray and beseech you in the Lord Jesus, that as you have received from us, how you ought to walk, and to please God, so also you would walk, that you may abound the more.
2 Gama kun san umarnan da muka ba ku ta wurin ikon Ubangiji Yesu.
For you know what precepts I have given to you by the Lord Jesus.
3 Nufin Allah ne a tsarkake ku, cewa ku guje wa fasikanci;
For this is the will of God, your sanctification; that you should abstain from fornication;
4 don kowannenku yă koya yadda zai ƙame kansa a hanyar da take mai tsarki, mai mutunci kuma,
That every one of you should know how to possess his vessel in sanctification and honour:
5 ba cikin muguwar sha’awa kamar ta marasa bangaskiya, waɗanda ba su san Allah ba;
Not in the passion of lust, like the Gentiles that know not God:
6 cikin wannan al’amari kuwa kada wani yă yi wa ɗan’uwansa laifi ko yă cuce shi. Ubangiji zai hukunta mutane saboda dukan irin waɗannan zunubai, kamar yadda muka riga muka gaya muku, muka kuma yi muku gargaɗi.
And that no man overreach, nor circumvent his brother in business: because the Lord is the avenger of all these things, as we have told you before, and have testified.
7 Gama Allah bai kira mu ga zaman marasa tsarki ba, sai dai ga zaman tsarki.
For God hath not called us unto uncleanness, but unto sanctification.
8 Saboda haka, duk wanda ya ƙi wannan umarni ba mutum ne ya ƙi ba sai ko Allah, wanda ya ba ku Ruhunsa Mai Tsarki.
Therefore, he that despiseth these things, despiseth not man, but God, who also hath given his holy Spirit in us.
9 Yanzu kuwa game da ƙaunar’yan’uwa, ba ma bukata mu rubuta muku, gama ku kanku Allah ya riga ya koya muku ku ƙaunaci juna.
But as touching the charity of brotherhood, we have no need to write to you: for yourselves have learned of God to love one another.
10 Gaskiyar kuwa ita ce, kuna ƙaunar dukan’yan’uwa ko’ina a Makidoniya. Duk da haka muna ƙara gargaɗe ku,’yan’uwa, ku yi haka sau da sau.
For indeed you do it towards all the brethren in all Macedonia. But we entreat you, brethren, that you abound more:
11 Ku mai da wannan burinku na yi natsattsiyar rayuwa, kuna mai da hankali ga sha’anin da yake gabanku, kuna kuma yin aiki da hannuwanku, kamar dai yadda muka gaya muku,
And that you use your endeavour to be quiet, and that you do your own business, and work with your own hands, as we commanded you:
12 don rayuwanku ta kullum ta zama da mutunci ga waɗanda suke na waje don kuma kada ku dogara a kan kowa.
and that you walk honestly towards them that are without; and that you want nothing of any man’s.
13 ’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege.
And we will not have you ignorant, brethren, concerning them that are asleep, that you be not sorrowful, even as others who have no hope.
14 Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu.
For if we believe that Jesus died, and rose again; even so them who have slept through Jesus, will God bring with him.
15 Bisa ga maganar Ubangiji kansa, muna gaya muku cewa mu da muke raye har yanzu, waɗanda aka bari har dawowar Ubangiji, tabbatacce ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba.
For this we say unto you in the word of the Lord, that we who are alive, who remain unto the coming of the Lord, shall not prevent them who have slept.
16 Gama Ubangiji kansa zai sauko daga sama, da umarni mai ƙarfi, da muryar babban mala’ika da kuma busar ƙahon Allah, waɗanda suka mutu kuwa cikin Kiristi za su tashi da farko.
For the Lord himself shall come down from heaven with commandment, and with the voice of an archangel, and with the trumpet of God: and the dead who are in Christ, shall rise first.
17 Bayan haka, mu da muke da rai da aka bari, za a ɗauke mu tare da su a cikin gizagizai don mu sadu da Ubangiji a sararin sama. Ta haka za mu kasance tare da Ubangiji har abada.
Then we who are alive, who are left, shall be taken up together with them in the clouds to meet Christ, into the air, and so shall we be always with the Lord.
18 Saboda haka ku ƙarfafa juna da waɗannan kalmomi.
Wherefore, comfort ye one another with these words.

< 1 Tessalonikawa 4 >