< 1 Tessalonikawa 4 >

1 A ƙarshe,’yan’uwa, mun umarce ku yadda za ku yi rayuwa domin ku gamshi Allah, kamar yadda kuke yi. Yanzu muna roƙonku muna kuma gargaɗe ku a cikin Ubangiji Yesu ku yi haka sau da sau.
Finally, then, brethren, we beseech and exhort you, by our Lord Jesus, that as you learned from us how you ought to walk and please God, you would abound more and more.
2 Gama kun san umarnan da muka ba ku ta wurin ikon Ubangiji Yesu.
For you know what commandments we gave you by our Lord Jesus.
3 Nufin Allah ne a tsarkake ku, cewa ku guje wa fasikanci;
For this is the will of God, your sanctification, that you keep yourselves from lewdness;
4 don kowannenku yă koya yadda zai ƙame kansa a hanyar da take mai tsarki, mai mutunci kuma,
That each one of you know how to keep his vessel in sanctification and in honor,
5 ba cikin muguwar sha’awa kamar ta marasa bangaskiya, waɗanda ba su san Allah ba;
not in passionate desire, as the Gentiles do, who know not God;
6 cikin wannan al’amari kuwa kada wani yă yi wa ɗan’uwansa laifi ko yă cuce shi. Ubangiji zai hukunta mutane saboda dukan irin waɗannan zunubai, kamar yadda muka riga muka gaya muku, muka kuma yi muku gargaɗi.
That no one take advantage of or injure his brother in this matter; because the Lord takes vengeance for all such things, as we also told you before, and fully testified:
7 Gama Allah bai kira mu ga zaman marasa tsarki ba, sai dai ga zaman tsarki.
for God has not called us for uncleanness, but for holiness.
8 Saboda haka, duk wanda ya ƙi wannan umarni ba mutum ne ya ƙi ba sai ko Allah, wanda ya ba ku Ruhunsa Mai Tsarki.
Therefore, he that despises, despises not man, but God, who has given us his Holy Spirit.
9 Yanzu kuwa game da ƙaunar’yan’uwa, ba ma bukata mu rubuta muku, gama ku kanku Allah ya riga ya koya muku ku ƙaunaci juna.
But with respect to brotherly love, you have no need that I write to you: for you yourselves are taught of God to love one another;
10 Gaskiyar kuwa ita ce, kuna ƙaunar dukan’yan’uwa ko’ina a Makidoniya. Duk da haka muna ƙara gargaɗe ku,’yan’uwa, ku yi haka sau da sau.
and indeed you do this to all the brethren that are in all Macedonia. But we exhort you, brethren, that you abound in love more and more,
11 Ku mai da wannan burinku na yi natsattsiyar rayuwa, kuna mai da hankali ga sha’anin da yake gabanku, kuna kuma yin aiki da hannuwanku, kamar dai yadda muka gaya muku,
and that you earnestly endeavor to live quietly, and that you attend to your own business, and work with your own hands, as we commanded you;
12 don rayuwanku ta kullum ta zama da mutunci ga waɗanda suke na waje don kuma kada ku dogara a kan kowa.
in order that you may walk with propriety toward those who are without, and may have need of nothing.
13 ’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege.
But concerning those who have fallen asleep, I would not have you ignorant, brethren, that you may not grieve, as others who have no hope.
14 Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu.
For if we believe that Jesus died and rose again, so also should we believe that God will, through Jesus, bring with him those who sleep.
15 Bisa ga maganar Ubangiji kansa, muna gaya muku cewa mu da muke raye har yanzu, waɗanda aka bari har dawowar Ubangiji, tabbatacce ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba.
For this we say to you by the word of the Lord, that we, the living, who remain till the coming of the Lord, shall not precede those who are asleep
16 Gama Ubangiji kansa zai sauko daga sama, da umarni mai ƙarfi, da muryar babban mala’ika da kuma busar ƙahon Allah, waɗanda suka mutu kuwa cikin Kiristi za su tashi da farko.
for the Lord himself will descend from heaven with a shout, with the voice of the archangel, and with the trump of God; and the dead in Christ shall arise first;
17 Bayan haka, mu da muke da rai da aka bari, za a ɗauke mu tare da su a cikin gizagizai don mu sadu da Ubangiji a sararin sama. Ta haka za mu kasance tare da Ubangiji har abada.
then we, the living who remain, shall, together with them, be caught up in clouds into the air to meet the Lord, and so shall we be ever with the Lord.
18 Saboda haka ku ƙarfafa juna da waɗannan kalmomi.
So, then, comfort one another with these words.

< 1 Tessalonikawa 4 >