< 1 Tessalonikawa 4 >
1 A ƙarshe,’yan’uwa, mun umarce ku yadda za ku yi rayuwa domin ku gamshi Allah, kamar yadda kuke yi. Yanzu muna roƙonku muna kuma gargaɗe ku a cikin Ubangiji Yesu ku yi haka sau da sau.
Finally therefore, brothers, we ask you, and summon in the Lord Jesus, that just as ye received from us how ye ought to walk and to please God, that ye may abound more.
2 Gama kun san umarnan da muka ba ku ta wurin ikon Ubangiji Yesu.
For ye know what commandments we gave you through the Lord Jesus.
3 Nufin Allah ne a tsarkake ku, cewa ku guje wa fasikanci;
For this is the will of God, your sanctification, for you to abstain from fornication,
4 don kowannenku yă koya yadda zai ƙame kansa a hanyar da take mai tsarki, mai mutunci kuma,
for each of you to know how to possess his own vessel in sanctification and reverence,
5 ba cikin muguwar sha’awa kamar ta marasa bangaskiya, waɗanda ba su san Allah ba;
not in passion of lust, as also the Gentiles who have not known God,
6 cikin wannan al’amari kuwa kada wani yă yi wa ɗan’uwansa laifi ko yă cuce shi. Ubangiji zai hukunta mutane saboda dukan irin waɗannan zunubai, kamar yadda muka riga muka gaya muku, muka kuma yi muku gargaɗi.
not to transgress and to cheat his brother in the affair, because the Lord is vengeful about all these things, as also we forewarned you and solemnly testified.
7 Gama Allah bai kira mu ga zaman marasa tsarki ba, sai dai ga zaman tsarki.
For God did not call us to uncleanness, but in sanctification.
8 Saboda haka, duk wanda ya ƙi wannan umarni ba mutum ne ya ƙi ba sai ko Allah, wanda ya ba ku Ruhunsa Mai Tsarki.
Therefore he who disregards, disregards not man, but God, who also gave his Holy Spirit to you.
9 Yanzu kuwa game da ƙaunar’yan’uwa, ba ma bukata mu rubuta muku, gama ku kanku Allah ya riga ya koya muku ku ƙaunaci juna.
But about brotherly love ye have no need to write to you, for ye yourselves are taught by God in order to love each other.
10 Gaskiyar kuwa ita ce, kuna ƙaunar dukan’yan’uwa ko’ina a Makidoniya. Duk da haka muna ƙara gargaɗe ku,’yan’uwa, ku yi haka sau da sau.
For ye are also doing it toward all the brothers in all Macedonia. But we exhort you, brothers, to abound more,
11 Ku mai da wannan burinku na yi natsattsiyar rayuwa, kuna mai da hankali ga sha’anin da yake gabanku, kuna kuma yin aiki da hannuwanku, kamar dai yadda muka gaya muku,
and to aspire to live quietly, and to do your own things, and to work with your own hands, just as we commanded you,
12 don rayuwanku ta kullum ta zama da mutunci ga waɗanda suke na waje don kuma kada ku dogara a kan kowa.
so that ye may walk properly toward those outside, and may have nothing lacking.
13 ’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege.
But we do not want you to be ignorant, brothers, about those who are asleep, so that ye may not grieve, as also the others who have no hope.
14 Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu.
For if we believe that Jesus died and arose, so also those who became asleep through Jesus, God will bring with him.
15 Bisa ga maganar Ubangiji kansa, muna gaya muku cewa mu da muke raye har yanzu, waɗanda aka bari har dawowar Ubangiji, tabbatacce ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba.
For this we say to you in the word of the Lord, that we who are alive, who remain for the coming of the Lord, will no, not precede those who became asleep.
16 Gama Ubangiji kansa zai sauko daga sama, da umarni mai ƙarfi, da muryar babban mala’ika da kuma busar ƙahon Allah, waɗanda suka mutu kuwa cikin Kiristi za su tashi da farko.
Because the Lord himself will descend from heaven with a shout, with a voice of the arch-agent, and with a trumpet of God. And the dead in Christ will rise first,
17 Bayan haka, mu da muke da rai da aka bari, za a ɗauke mu tare da su a cikin gizagizai don mu sadu da Ubangiji a sararin sama. Ta haka za mu kasance tare da Ubangiji har abada.
then we who are alive, who remain, will be caught up simultaneously with them in clouds to the Lord's gathering in the air. And so we will always be with the Lord.
18 Saboda haka ku ƙarfafa juna da waɗannan kalmomi.
Therefore encourage each other with these words.