< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
Bhai khan, kele koile apnikhan nijor jani ase amikhan pora apnikhan logote aha to ene misa-misi pora nohoi.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
Hoile bhi, apnikhan nije jana nisena, amikhan poila bhi dukh paise aru Philippi sheher te sorom khaise. Amikhan Isor logote mon dangor kori kene bisi dukh pora Isor laga kotha prochar korise.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
Kilekoile amikhan pora utsah diya khan galti pora nohoi, letera thaka pora nohoi, nohoile thogabole nimite bhi nohoi.
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
Hoilebi jineka Isor pora amikhan ke Tai laga susamachar dise, etu nimite manu ke khushi kori bole karone amikhan kotha kuwa nohoi, kintu Isor kun pora manu laga mon sai Taike khushi kori bole koi ase.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
Kilekoile apuni khan jane amikhan to phusla bole, nohoile misa kotha pora kiba lobole aha nohoi - Isor he amikhan laga sakhi ase.
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
Amikhan manu pora proshansa bisara nohoi, apuni khan pora aru dusra khan pora bhi.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
Amikhan Khrista laga chela ase koi kene apnikhan uporte bhari boja nisena ahibo paribo thakise. Kintu, apnikhan majote, amikhan he bacha nisena hoi jaise aru ama pora jineka bacha khan ke morom kore,
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
etu nisena apnikhan ke bisi morom korise. Khali Isor laga kotha he nohoi hoilebi nijor jibon bhi dibole taiyar ase. Kelemane apuni khan karone bisi morom hoi jaise.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
Kilekoile bhai khan, amikhan dukh pora kaam kora to apnikhan jani ase. Amikhan Isor laga kotha apnikhan ke kowa somoite, apnikhan ke dukh kosto nadibo nimite amikhan din raat kaam korise.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Apnikhan aru Isor bhi sakhi ase, amikhan laga niyom to biswasi khan age te kiman pobitro aru dharmik thakise.
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
Etu nisena amikhan kineka apnikhan logote thakise etu apnikhan jani ase, jineka ekjon baba tai laga nijor bacha logote thake,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
etu nisena apuni khan ke mon uthai dise, mon dangor kori dise aru, kineka korile Isor ke khushi koribo eitu khan hodai sikhai thakise, jun pora apnikhan ke tai laga rajyo aru mohima te matise.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
Etu nimite amikhan bhi Isor ke hodai dhanyavad diye, jitia apnikhan Isor luwa somoite juntu amikhan hunise, apuni khan etu ke manu laga kotha ase bhaba nai, kintu jineka Isor laga kotha hosa ase, jun biswas kore eitu khan logote kaam kori bole hoise.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
Kelemane, apuni, bhai khan, Judea te Isor laga girja laga chela hoi jaise juntu Khrista Jisu te ase. Aru kineka taikhan ke dukh kosto dise, apuni khan bhi nijor manu khan pora dukh kosto dise, jineka taikhan ke Yehudi jati khan pora dise,
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
jun khan pora Probhu Jisu aru tai laga bhabobadi khan ke morai dise, aru amikhan ke bhi khedai dise. Utu Yehudi khan pora Isor ke khushi kori bole napare. Ulta, taikhan manu khan logote dushman hoi jaise.
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
Amikhan ke Porjati khan logote jai kene bachai diya laga kotha rukhai thake, eitu khan nijor laga paap ke aru bhi bisi kori diye. Kintu hekh dinte Isor laga khong taikhan uporte ahibo.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
Kintu bhai khan, olop din karone amikhan ke apnikhan pora alag kori dise, kintu gaw pora hoise, mon pora nohoi. Amikhan apnikhan ke bisi sabole mon ase.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Kilekoile amikhan apnikhan ke lok kori bole bisi itcha thakise, moi nije Paul, bhi ek duibar nisena- kintu Saitan pora amikhan ke rukhai dise.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
Kilekoile Probhu Jisu wapas aha somoite, amikhan laga asha aru itcha, nohoile khushi laga mukut kun ase? Etu apnikhan nohoi naki?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
Kilekoile apnikhan he amikhan laga shaan aru khushi ase.

< 1 Tessalonikawa 2 >