< 1 Tessalonikawa 2 >
1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
Vous savez vous-mêmes, frères, que notre venue parmi vous n’a pas été sans fruits.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
Mais après avoir souffert et subi des outrages à Philippes, comme vous le savez, nous vînmes pleins de confiance en notre Dieu, vous prêcher hardiment son Evangile, au milieu de bien des luttes.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
Car notre prédication n’a pas procédé de l’erreur, ni d’une intention vicieuse, ni de fraude aucune;
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
mais, selon que Dieu nous a jugés dignes de nous confier l’Evangile, ainsi enseignons-nous, non comme pour plaire à des hommes, mais à Dieu, qui sonde nos cœurs.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
Jamais, en effet, nos discours n’ont été inspirés par la flatterie, comme vous le savez, ni par un motif de cupidité, Dieu en est témoin.
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
La gloire humaine, nous ne l’avons recherchée ni de vous ni de personne;
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
alors que nous aurions pu, comme apôtres du Christ, prétendre à quelque autorité, nous avons été au contraire plein de condescendance au milieu de vous. Comme une nourrice entoure de tendres soins ses enfants,
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
ainsi, dans notre affection pour vous, nous aurions voulu vous donner, non seulement l’Evangile de Dieu, mais notre vie même, tant vous nous étiez devenus chers.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
Vous vous rappelez, frères, notre labeur et nos fatigues: c’est en travaillant nuit et jour, pour n’être à charge à personne d’entre vous, que nous vous avons prêché l’Evangile de Dieu.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Vous êtes témoins, et Dieu aussi, combien sainte, juste et irrépréhensible a été notre conduite envers vous qui croyez;
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
comment, ainsi que vous le savez, nous avons été pour chacun de vous ce qu’un père est pour ses enfants,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
vous priant, vous exhortant, vous conjurant de marcher d’une manière digne de Dieu, qui vous appelle à son royaume et à sa gloire.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
C’est pourquoi nous aussi, nous ne cessons de rendre grâces à Dieu, de ce qu’ayant reçu la divine parole que nous avons fait entendre, vous l’avez reçue, non comme parole des hommes, mais, ainsi qu’elle l’est véritablement, comme une parole de Dieu. C’est elle qui déploie sa puissance en vous qui croyez.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
Car vous, frères, vous êtes devenus les imitateurs des Eglises de Dieu qui se réunissent en Jésus-Christ dans la Judée, puisque vous avez souffert vous aussi de la part de vos compatriotes, ce qu’elles ont eu à souffrir de la part des Juifs, —
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
de ces Juifs qui ont mis à mort le Seigneur Jésus et les prophètes, nous ont persécutés, ne plaisent pas à Dieu et sont ennemis du genre humain,
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
nous empêchant de prêcher aux nations pour leur salut: de sorte qu’ils comblent sans cesse la mesure de leurs péchés. Mais la colère de Dieu est tombée sur eux pour y demeurer jusqu’à la fin.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
Pour nous, frères, un instant tristement séparés de vous, de corps, non de cœur, nous avions grande hâte et un vif désir de vous revoir.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Aussi voulions-nous vous aller trouver, en particulier, moi, Paul, une première et une seconde fois; mais Satan nous en a empêchés.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
Quelle est, en effet, notre espérance, notre joie, notre couronne de gloire? N’est-ce pas vous qui l’êtes, devant notre Seigneur Jésus, pour le jour de son avènement?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
Oui, c’est vous qui êtes notre gloire et notre joie.