< 1 Tessalonikawa 2 >
1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
For ye yourselves, brethren, know our entrance among you, that it was not in vain.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
But though we had suffered before and been injuriously treated, as ye know, at Philippi, we spake boldly in the name of our God to declare unto you the gospel of God with much conflict.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
For our exhortation was not of deceit, nor of impurity, nor in guile:
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
but as we have been approved by God to be entrusted with the gospel, so we speak, not as pleasing men, but God, who trieth our hearts.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
For neither at any time used we flattering speech, as ye know, nor covetous pretence, God is witness:
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
nor sought we glory of men, neither of you, nor of others: though we might have expected maintenance, as the apostles of Christ.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
But we were gentle among you, even as a nurse cherisheth her children:
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
so we, being affectionately desirous of you, were willing to impart to you, not only the gospel of God, but even our own souls, because ye were dear unto us.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
For ye remember, brethren, our labor and toil; for working night and day, that we might not be burthensome to any of you, we preached among you the gospel of God.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Ye are witnesses, and God also, how holily, and justly, and unblameably we behaved towards you that believe:
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
as ye know likewise, how we exhorted and comforted every one of you, as a father his children;
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
and charged you, that ye should walk worthy of God, who hath called you to his kingdom and glory.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
For this also we thank God continually, that when ye received the word of God, which ye heard from us, ye received it not as the word of men, but (as it is in truth) the word of God, which also worketh effectually in you that believe.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For ye, brethren, became followers of the churches of God, which are in Judea, in Christ Jesus, in that ye also have suffered the same things from your own countrymen, as they have from the Jews:
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
who both killed the Lord Jesus, and their own prophets, and have persecuted us; who are displeasing to God, and contrary to all men:
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
forbidding us to speak to the Gentiles that they might be saved, thus going on to fill up their sins perpetually: but wrath is coming upon them to extremity.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
But we, brethren, being separated from you for a season, in person not in heart, endeavoured the more earnestly to see you again with much desire.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Wherefore we would have come unto you (even I Paul) once and again; but Satan hindered us.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what is our hope, or joy, or crown of boasting? are not ye also among others in the presence of our Lord Jesus Christ at his coming?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
for ye are our glory and our joy.