< 1 Tessalonikawa 2 >
1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
For yourselves, brothers, know our entrance in to you, that it was not in vain:
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
But even after that we had suffered before, and were shamefully entreated, as you know, at Philippi, we were bold in our God to speak to you the gospel of God with much contention.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
For our exhortation was not of deceit, nor of uncleanness, nor in guile:
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
But as we were allowed of God to be put in trust with the gospel, even so we speak; not as pleasing men, but God, which tries our hearts.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
For neither at any time used we flattering words, as you know, nor a cloak of covetousness; God is witness:
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
Nor of men sought we glory, neither of you, nor yet of others, when we might have been burdensome, as the apostles of Christ.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
But we were gentle among you, even as a nurse cherishes her children:
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
So being affectionately desirous of you, we were willing to have imparted to you, not the gospel of God only, but also our own souls, because you were dear to us.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
For you remember, brothers, our labor and travail: for laboring night and day, because we would not be chargeable to any of you, we preached to you the gospel of God.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
You are witnesses, and God also, how piously and justly and blamelessly we behaved ourselves among you that believe:
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
As you know how we exhorted and comforted and charged every one of you, as a father does his children,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
That you would walk worthy of God, who has called you to his kingdom and glory.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
For this cause also thank we God without ceasing, because, when you received the word of God which you heard of us, you received it not as the word of men, but as it is in truth, the word of God, which effectually works also in you that believe.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For you, brothers, became followers of the churches of God which in Judaea are in Christ Jesus: for you also have suffered like things of your own countrymen, even as they have of the Jews:
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
Who both killed the Lord Jesus, and their own prophets, and have persecuted us; and they please not God, and are contrary to all men:
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
Forbidding us to speak to the Gentiles that they might be saved, to fill up their sins always: for the wrath is come on them to the uttermost.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
But we, brothers, being taken from you for a short time in presence, not in heart, endeavored the more abundantly to see your face with great desire.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Why we would have come to you, even I Paul, once and again; but Satan hindered us.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what is our hope, or joy, or crown of rejoicing? Are not even you in the presence of our Lord Jesus Christ at his coming?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
For you are our glory and joy.