< 1 Tessalonikawa 2 >
1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
For you yourselves know, brethren, our entrance among you, that it was not in vain.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
But having suffered before, and having been outraged, as you know, in Philippi, we were bold in our God to speak to you the gospel of God in the midst of great peril.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
For our exhortation arose not from deception, nor from uncleanness, nor was it with guile;
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
but as God had judged us worthy to be intrusted with the gospel, so we speak, not as pleasing men, but God, who tries our hearts.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
For neither nattering words did we at any time use, as you know, nor a pretext for covetousness; God is witness:
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
nor did we seek glory from men, neither from you nor from others; though we could have been burdensome as the apostles of Christ.
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
But we were gentle among you. As a nurse nourishes her children,
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
so, having a strong affection for you, we were well pleased to impart to you not only the gospel of God, but our own lives also, because you had become dear to us.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
For you remember, brethren, our labor and toil; for, laboring night and day, that we might not be burdensome to any one of you, we preached to you the gospel of God.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
You are witnesses, and God also, in how holy and just and blameless a manner we conducted ourselves among you that believe,
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
as indeed you know how we exhorted and comforted and charged every one of you, as a father his children,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
that you should walk in a manner worthy of God, who has called you to his own kingdom and glory.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
For this reason, also, we thank God without ceasing; because, when you received the word of God, as preached by us, you embraced it, not as the word of men, but, as it is in truth, the word of God, which effectually works in you that believe.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For you, brethren, became imitators of the churches of God in Judea which are in Christ Jesus; for you, also, have suffered the same things from your own countrymen, that they have suffered from the Jews,
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
who both killed the Lord Jesus and the prophets, and have persecuted us, and do not please God, and are opposed to all men,
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
forbidding us to speak to the Gentiles that they may be saved, in order that they may fill up their sins at all times: but the wrath is coming upon them to the full.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
But we, brethren, having been taken from you for a short time, in person, not in heart, did, with great desire, endeavor the more earnestly to see your face.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
For this reason, we intended to go to you, (I Paul) both once and again, but Satan hindered us.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what is our hope, or joy, or crown of rejoicing? Are not even you, in the presence of our Lord Jesus Christ at his coming?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
You indeed are our glory and joy.