< 1 Tessalonikawa 2 >
1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
For ye yourselves know, brothers, our entrance with you, that it has not become empty.
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
But having suffered before and been mistreated in Philippi, as ye know, we were bold in our God to speak to you the good news of God within much conflict.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
For our exhortation is not from error, nor from uncleanness, nor in deception,
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
but as we have been approved by God to be entrusted with the good news, thus we speak, not as pleasing men, but God who proves our hearts.
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
For we came neither in word of flattery (at any time as ye know) nor a pretense of greed (God is witness)
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
nor seeking glory from men, neither from you nor from others. While able to bear down as apostles of Christ,
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
nevertheless we became gentle in the midst of you, as a nurse cherishes her own children.
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
Thus being desirous of you, we were pleased to impart to you, not only the good news of God, but also our own souls, because ye have become beloved to us.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
For ye remember, brothers, our labor and the hardship. For, laboring night and day in order not to burden any of you, we preached to you the good news of God.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Ye are witnesses, and God, how piously and justly and blamelessly we became to you who believe,
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
just as ye know, as each one of you as a father of his own children, imploring you, and comforting,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
and solemnly declaring for you to walk worthily of God, who calls you into his own kingdom and glory.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
And because of this we thank God without ceasing, because, having received the word of God heard from us, ye received not the word of men, but as it truly is, the word of God, which also is at work in you who believe.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
For ye, brothers, became imitators of the congregations of God, which are in Judea in Christ Jesus, because ye also suffered the same things by your own countrymen, just as also they by the Jews.
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
The men who both killed the Lord Jesus and their own prophets, and who persecuted us, and are not pleasing to God, and are contrary to all men.
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
Forbidding us to speak to the Gentiles so that they might be saved, in order to fill up their sins always. But wrath came upon them finally.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
But we, brothers, who were orphaned from you for the time of an hour, in presence not in heart, hastened more earnestly to see your face, with much desire.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Therefore we wanted to come to you, indeed I, Paul, even once and again, and Satan hindered us.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
For what is our hope or joy or crown of boast? Or is it not even ye, before our Lord Jesus at his coming?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
For ye are our glory and joy.