< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
Защото сами вие знаете, братя, че нашия достъп при вас не беше напразно;
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
но както бяхме от по напред пострадали и бяхме опозо рени във Филипи, както знаете, одързостихме се в нашия Бог да ви проповядваме Божието Благовевстие всред голяма борба.
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
Защото в нашето увещание не е имало самоизмама, нито нечисто подбуждение, нито е било с лукавщина;
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
но както сме били одобрени, от Бога да ни повери делото на благовестието, така говорим, не като да угождаваме на човеците, а на Бога, Който изпитва сърцата ни
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
Защото, както знаете, никога не сме употребявали ласкателни думи, или прикрито сребролюбие, (Бог е свидетел);
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
нито сме търсили слава от човеци, било от вас или от други, (ако и да сме могли да притежаваме власт като Христови апостоли),
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
но сме били нежни поради вас, както доилка, когато се грижи за чадата си.
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
Така, като имахме гореща любов към вас, беше ни драго да ви предадем не само Божието благовестие, но и своите души, защото ни бяхте станали мили.
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
Затова Вие, братя, помните нашия труд и усилие, как работещи денем и нощем, за да не отеготим ни един от вас, проповядвахме ви Божието благовестие.
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
Вие сте свидетели, и Бог, как свето, праведно и неукорно се обхождахме към вас, вярващите,
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
като знаете как увещавахме и утешавахме всеки един от вас, като баща чедата си,
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
и ви заръчахме да се обхождате достойно за Бога, Който ви призовава в Своето царство и слава.
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
И за туй и ние непрестанно благодарим на Бога загдето, като приехте чрез нас словото на Божието послание, приехте го, не като човешко слово, а като Божие слово, каквото е наистина, което и действува между вас, вярващите.
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
Защото вие, братя, станахте подражатели на Божииите в Христа Исуса църкви, които са в Юдея, понеже вие пострадахте същото от своите сънародници, както и от юдеите;
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
които и Господа Исуса и пророците убиха, и нас прогониха, на Бога не угождават и на всичките човеци са противни,
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
като ни забраняват да говорим на езичниците, за да се спасят. Така те допълнят мярката на греховете си; но безграничният гняв ги постигна.
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
А ние, братя, като осиротяхме от вас за малко време, (колкото за телесно присъствие, а не по сърце), постарахме се още повече, с голямо желание, дано видим лицето ви.
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
Защото поискахте да дойдем при вас (поне аз Павел) един два пъти, но сатана ни попречи.
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
Понеже коя е нашата надежда, или радост, или венец, с който се хвалим? Не сте ли вие, пред нашия Господ Исус при неговото пришествие?
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
Защото вие сте нашата слава и радост.

< 1 Tessalonikawa 2 >