< 1 Tessalonikawa 2 >

1 Kun sani,’yan’uwa, cewa ziyararmu a gare ku ba tă zama a banza ba.
ܘܐܢܬܘܢ ܝܕܥܝܢ ܐܢܬܘܢ ܐܚܝ ܕܡܥܠܢܢ ܕܠܘܬܟܘܢ ܠܐ ܗܘܐ ܤܪܝܩܐܝܬ ܗܘܐ
2 Mun riga mun sha wahala, aka kuma zage mu a Filibbi, kamar yadda kuka sani, amma da taimakon Allahnmu muka yi ƙarfin hali muka sanar muku bishararsa duk da matsananciyar gāba.
ܐܠܐ ܠܘܩܕܡ ܚܫܢܢ ܘܐܨܛܥܪܢܢ ܐܝܟ ܕܝܕܥܝܬܘܢ ܒܦܝܠܝܦܘܤ ܘܗܝܕܝܢ ܒܐܓܘܢܐ ܪܒܐ ܡܠܠܢ ܥܡܟܘܢ ܒܦܪܗܤܝܐ ܕܐܠܗܢ ܤܒܪܬܗ ܕܡܫܝܚܐ
3 Gama roƙon da muke yi bai fito daga kuskure ko munafunci ba, ba kuwa ƙoƙari muke yi mu yaudare ku ba.
ܒܘܝܐܢ ܓܝܪ ܠܐ ܗܘܐ ܡܢ ܛܥܝܘܬܐ ܐܦܠܐ ܡܢ ܛܢܦܘܬܐ ܐܦܠܐ ܒܢܟܠܐ
4 A maimako haka, muna magana ne kamar mutanen da Allah ya amince yă danƙa musu amanar wannan bishara. Ba ma ƙoƙari mu gamshi mutane sai dai Allah, mai auna zukatanmu.
ܐܠܐ ܐܝܟ ܡܐ ܕܒܩܝܢܢ ܠܐܠܗܐ ܕܬܬܗܝܡܢ ܤܒܪܬܗ ܗܟܢܐ ܡܡܠܠܝܢܢ ܠܐ ܐܝܟ ܕܠܒܢܝ ܐܢܫܐ ܢܫܦܪ ܐܠܐ ܠܐܠܗܐ ܗܘ ܕܒܩܐ ܠܒܘܬܢ
5 Kun san ba ma taɓa yin daɗin baki ko mu yi ƙoƙarin kasance da halin kwaɗayin da muke ɓoyewa, Allah shi ne shaidarmu.
ܐܦܠܐ ܓܝܪ ܡܡܬܘܡ ܐܬܚܫܚܢ ܒܡܡܠܠܐ ܫܕܠܐ ܐܝܟ ܕܝܕܥܝܢ ܐܢܬܘܢ ܘܠܐ ܒܥܠܬܐ ܕܝܥܢܘܬܐ ܐܠܗܐ ܤܗܕ
6 Ba ma neman yabo daga wurin mutane, ko a gare ku, ko ga waɗansu. A matsayinmu na manzannin Kiristi da mun so, da mun nawaita muku,
ܘܠܐ ܒܥܝܢ ܫܘܒܚܐ ܡܢ ܒܢܝܢܫܐ ܠܐ ܡܢܟܘܢ ܘܠܐ ܡܢ ܐܚܪܢܐ ܟܕ ܡܫܟܚܝܢ ܗܘܝܢ ܝܩܝܪܐ ܠܡܗܘܐ ܐܝܟ ܫܠܝܚܐ ܕܡܫܝܚܐ
7 amma muka kasance masu sauƙinkai a cikinku, kamar yadda mahaifiya take lura da ƙananan’ya’yanta.
ܐܠܐ ܗܘܝܢ ܒܝܢܬܟܘܢ ܡܟܝܟܐ ܘܐܝܟ ܡܪܒܝܢܝܬܐ ܕܡܚܒܒܐ ܒܢܝܗ
8 Muka ƙaunace ku ƙwarai har muka ji daɗin bayyana muku, ba bisharar Allah kaɗai ba amma har rayukanmu ma, domin kun zama ƙaunatattu a gare mu.
ܗܟܢܐ ܐܦ ܚܢܢ ܡܚܒܒܝܢܢ ܘܡܤܘܚܝܢܢ ܠܡܬܠ ܠܟܘܢ ܠܐ ܒܠܚܘܕ ܤܒܪܬܗ ܕܐܠܗܐ ܐܠܐ ܐܦ ܢܦܫܢ ܡܛܠ ܕܚܒܝܒܝܢ ܐܢܬܘܢ
9 Ba shakka kuna iya tunawa,’yan’uwa, famarmu da kuma wahalarmu; mun yi aiki dare da rana don kada mu zama nauyi wa wani yayinda muke muku wa’azin bisharar Allah.
ܥܗܕܝܢ ܐܢܬܘܢ ܓܝܪ ܐܚܝܢ ܕܠܐܝܢ ܗܘܝܢ ܘܥܡܠܝܢ ܒܥܒܕ ܐܝܕܝܢ ܒܠܠܝܐ ܘܒܐܝܡܡܐ ܕܥܠ ܚܕ ܡܢܟܘܢ ܠܐ ܢܐܩܪ
10 Ku shaidu ne, haka ma Allah, na yadda muka yi zaman tsarki, adalci da kuma marar aibi a cikinku, ku da kuka ba da gaskiya.
ܐܢܬܘܢ ܤܗܕܝܢ ܘܐܠܗܐ ܐܝܟܢܐ ܐܟܪܙܢ ܠܟܘܢ ܤܒܪܬܗ ܕܐܠܗܐ ܕܟܝܐܝܬ ܘܟܐܢܐܝܬ ܘܕܠܐ ܪܫܝܢ ܗܘܝܢ ܠܘܬ ܟܠܗܘܢ ܡܗܝܡܢܐ
11 Gama kun san cewa mun bi da kowannenku yadda mahaifi yakan yi da’ya’yansa,
ܐܝܟܢܐ ܕܝܕܥܝܢ ܐܢܬܘܢ ܕܡܢ ܚܕ ܚܕ ܡܢܟܘܢ ܐܝܟ ܐܒܐ ܡܢ ܒܢܘܗܝ ܒܥܝܢ ܗܘܝܢ ܘܡܠܝܢ ܗܘܝܢ ܒܠܒܟܘܢ ܘܡܤܗܕܝܢܢ ܠܟܘܢ
12 muna ƙarfafa ku, muna ta’azantar da ku, muna kuma gargaɗe ku ku yi rayuwar da za tă cancanci Allah, wanda ya kira ku zuwa mulkinsa da kuma ɗaukakarsa.
ܕܬܗܠܟܘܢ ܐܝܟ ܕܝܐܐ ܠܐܠܗܐ ܗܘ ܕܩܪܟܘܢ ܠܡܠܟܘܬܗ ܘܠܫܘܒܚܗ
13 Muna kuma gode wa Allah ba fasawa domin, sa’ad da kuka karɓi maganar Allah, wadda kuka ji daga gare mu, kun karɓe ta ba kamar maganar mutane ba, sai dai kamar yadda take, maganar Allah wadda take aiki a cikinku ku da kuka ba da gaskiya.
ܡܛܠ ܗܢܐ ܐܦ ܚܢܢ ܡܘܕܝܢܢ ܐܡܝܢܐܝܬ ܠܐܠܗܐ ܕܡܠܬܐ ܕܐܠܗܐ ܕܩܒܠܬܘܢ ܡܢܢ ܠܐ ܗܘܐ ܐܝܟ ܡܠܬܐ ܕܒܢܝܢܫܐ ܩܒܠܬܘܢܗ ܐܠܐ ܐܝܟܢܐ ܕܐܝܬܝܗ ܫܪܝܪܐܝܬ ܡܠܬܐ ܕܐܠܗܐ ܘܗܝ ܒܥܒܕܐ ܡܤܬܥܪܐ ܒܟܘܢ ܒܐܝܠܝܢ ܕܡܗܝܡܢܝܢ
14 Gama ku,’yan’uwa, kun zama masu koyi da ikkilisiyoyin Allah a Yahudiya waɗanda suke cikin Kiristi Yesu. Kun sha wahala a hannun mutanen ƙasarku kamar yadda ikkilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa,
ܐܢܬܘܢ ܕܝܢ ܐܚܝ ܐܬܕܡܝܬܘܢ ܠܥܕܬܐ ܕܐܠܗܐ ܕܒܝܗܘܕ ܗܠܝܢ ܕܒܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܕܗܟܢ ܤܝܒܪܬܘܢ ܐܦ ܐܢܬܘܢ ܡܢ ܒܢܝ ܫܪܒܬܟܘܢ ܐܝܟܢܐ ܕܐܦ ܗܢܘܢ ܡܢ ܝܗܘܕܝܐ
15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa suka kuma kore mu. Ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuwa da dukan mutane
ܗܢܘܢ ܕܠܡܪܢ ܝܫܘܥ ܡܫܝܚܐ ܩܛܠܘ ܘܠܢܒܝܐ ܕܡܢܗܘܢ ܘܠܢ ܪܕܦܘ ܘܠܐܠܗܐ ܠܐ ܫܦܪܝܢ ܘܥܒܝܕܝܢ ܤܩܘܒܠܐ ܠܟܠܗܘܢ ܒܢܝ ܐܢܫܐ
16 suna ƙoƙarin hana mu yin magana ga Al’ummai don kada su sami ceto. Ta haka kullum suke ƙara tara tsibin zunubansu. Fushin Allah ya aukar musu a ƙarshe.
ܕܟܠܝܢ ܠܢ ܕܢܡܠܠ ܥܡ ܥܡܡܐ ܕܢܚܘܢ ܠܡܫܠܡܘ ܚܛܗܝܗܘܢ ܒܟܠܙܒܢ ܡܛܝ ܕܝܢ ܥܠܝܗܘܢ ܪܘܓܙܐ ܥܕܡܐ ܠܚܪܬܐ
17 Amma,’yan’uwa, sa’ad da aka raba mu da ku na ɗan lokaci (a jiki, ba a tunani ba), daga cikin marmarinmu mai tsanani mun yi duk abin da muke iya yi mu gan ku.
ܚܢܢ ܕܝܢ ܐܚܝܢ ܗܘܝܢ ܝܬܡܐ ܡܢܟܘܢ ܙܒܢܐ ܕܫܥܬܐ ܒܐܦܝܢ ܘܠܐ ܒܠܒܢ ܘܝܬܝܪܐܝܬ ܐܬܚܦܛܢ ܠܡܚܙܐ ܐܦܝܟܘܢ ܒܚܘܒܐ ܤܓܝܐܐ
18 Gama mun so mu zo wurinku, tabbatacce ni, Bulus, na yi ƙoƙari sau da sau, amma Shaiɗan ya hana mu.
ܘܨܒܝܢ ܕܢܐܬܐ ܠܘܬܟܘܢ ܐܢܐ ܦܘܠܘܤ ܚܕܐ ܙܒܢ ܘܬܪܬܝܢ ܘܥܘܟܢܝ ܤܛܢܐ
19 Gama mene ne begenmu, farin cikinmu, ko kuma rawanin da zai zama mana abin ɗaukaka a gaban Ubangijinmu Yesu sa’ad da ya dawo? Ba ku ba ne?
ܐܝܢܘ ܓܝܪ ܤܒܪܢ ܘܚܕܘܬܢ ܘܟܠܝܠܐ ܕܫܘܒܗܪܢ ܐܠܐ ܐܢ ܐܢܬܘܢ ܩܕܡ ܡܪܢ ܝܫܘܥ ܒܡܐܬܝܬܗ
20 Tabbatacce, ku ne ɗaukakarmu da kuma farin cikinmu.
ܐܢܬܘܢ ܐܢܘܢ ܓܝܪ ܬܫܒܘܚܬܢ ܘܚܕܘܬܢ

< 1 Tessalonikawa 2 >