< 1 Tessalonikawa 1 >
1 Bulus, Sila da Timoti, Zuwa ga ikkilisiyar Tessalonikawa ta Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi. Alheri da salama su kasance tare da ku.
Paulus, Silvanus und Timotheus begrüßen die Gemeinde in Thessalonich, die mit Gott dem Vater und dem Herrn Jesus Christus in Gemeinschaft steht. Gnade sei mit euch und Friede!
2 Kullum muna gode wa Allah dominku duka, muna ambatonku cikin addu’o’inmu.
Wir danken Gott allezeit für euch alle, indem wir euer in unseren Gebeten gedenken.
3 Muna tunawa da aikinku ba fasawa a gaban Allah da Ubanmu ta wurin bangaskiya, da famar da kuke yi domin ƙauna, da kuma begenku marar gushewa ga Ubangijinmu Yesu Kiristi.
Denn fort und fort erinnern wir uns vor dem Angesicht unseres Gottes und Vaters an eure Arbeit im Glauben, eure Mühe in der (brüderlichen) Liebe und eure Ausdauer in der Hoffnung (auf das Kommen) unseres Herrn Jesus Christus.
4 Gama mun sani,’yan’uwa, ƙaunatattu na Allah, cewa ya zaɓe ku,
Wir wissen ja, von Gott geliebte Brüder, daß ihr auserwählt seid.
5 domin bishararmu ba tă zo gare ku da kalmomi kawai ba, amma da iko, da Ruhu Mai Tsarki, da kuma cikakken tabbaci. Kun san irin rayuwar da muka yi a cikinku don amfaninku.
Denn wir haben die Heilsbotschaft nicht nur mit Worten bei euch verkündigt, sondern auch in Kraft und im Heiligen Geist und mit großer Glaubenszuversicht. Es ist euch wohlbekannt, wie wir zu euerm Besten unter euch gewirkt haben.
6 Har kuka zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji; duk da tsananin wahala, kuka karɓi saƙon nan da farin ciki wanda Ruhu Mai Tsarki ya bayar.
Und ihr seid uns und dem Herrn nachgefolgt. Denn trotz vieler Trübsal habt ihr mit jener Freude, die der Heilige Geist wirkt, das Wort aufgenommen,
7 Ta haka kuwa kuka zama gurbi ga dukan masu bi a Makidoniya da Akayya.
so daß ihr für alle Gläubigen in Mazedonien und Achaja ein Vorbild geworden seid.
8 Saƙon Ubangiji ya fito daga gare ku ne ba a Makidoniya da Akayya kaɗai ba bangaskiyarku ga Allah ta zama sananne ko’ina. Saboda haka ba ma bukata mu faɗa wani abu a kai,
Denn von euch ist das Wort des Herrn (wie ein Posaunenhall) ausgegangen, und nicht nur in Mazedonien und Achaja, sondern überall ist euer Glaube an Gott bekannt geworden. Darum brauchen wir auch (zu anderen) nicht weiter darüber zu reden.
9 gama su kansu su suke ba da labari irin karɓar da kuka yi mana. Suna faɗin yadda kuka juyo ga Allah daga gumaka don ku bauta wa Allah rayayye da kuma na gaskiya,
Denn alle (die von euch sprechen) erzählen aus freien Stücken, welche (gastliche) Aufnahme wir bei euch gefunden, und wie ihr euch von den Abgöttern zu Gott bekehrt habt, um ihm, dem lebendigen, wahren Gott, zu dienen
10 ku kuma jira dawowar Ɗansa daga sama, wanda ya tasa daga matattu, Yesu, wanda ya cece mu daga fushi mai zuwa.
und seinen Sohn, den er von den Toten auferweckt hat, vom Himmel zu erwarten — Jesus, der uns vor dem kommenden Zorngericht bewahrt.