< 1 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, Sila da Timoti, Zuwa ga ikkilisiyar Tessalonikawa ta Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi. Alheri da salama su kasance tare da ku.
Paul, Silvanus and Timothy, to the congregation of Thessalonians in God the Father and Sovereign Jesus Christ: Grace and peace to you from God our Father and Sovereign Jesus Christ.
2 Kullum muna gode wa Allah dominku duka, muna ambatonku cikin addu’o’inmu.
We always give thanks to God for all of you, making mention of you in our prayers,
3 Muna tunawa da aikinku ba fasawa a gaban Allah da Ubanmu ta wurin bangaskiya, da famar da kuke yi domin ƙauna, da kuma begenku marar gushewa ga Ubangijinmu Yesu Kiristi.
continually remembering before our God and Father your work for the Faith and your labor coming from the Love and your perseverance based on the Hope, our Lord Jesus Christ being their source,
4 Gama mun sani,’yan’uwa, ƙaunatattu na Allah, cewa ya zaɓe ku,
knowing as we do, brothers loved by God, that you are chosen.
5 domin bishararmu ba tă zo gare ku da kalmomi kawai ba, amma da iko, da Ruhu Mai Tsarki, da kuma cikakken tabbaci. Kun san irin rayuwar da muka yi a cikinku don amfaninku.
You see, our Gospel did not come to you in word only, but also in power and in the Holy Spirit and with complete certainty (of course you know what sort of men we proved to be among you for your sake).
6 Har kuka zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji; duk da tsananin wahala, kuka karɓi saƙon nan da farin ciki wanda Ruhu Mai Tsarki ya bayar.
Yes you became imitators of us and of the Lord, having received the Word with the Holy Spirit's joy, in spite of severe affliction,
7 Ta haka kuwa kuka zama gurbi ga dukan masu bi a Makidoniya da Akayya.
so that you became examples to all the believers in Macedonia and Achaia.
8 Saƙon Ubangiji ya fito daga gare ku ne ba a Makidoniya da Akayya kaɗai ba bangaskiyarku ga Allah ta zama sananne ko’ina. Saboda haka ba ma bukata mu faɗa wani abu a kai,
That is because the Word of the Lord sounded out from you, not only in Macedonia and Achaia but also in every place—your faith toward God has gone forth, so that we do not need to say anything.
9 gama su kansu su suke ba da labari irin karɓar da kuka yi mana. Suna faɗin yadda kuka juyo ga Allah daga gumaka don ku bauta wa Allah rayayye da kuma na gaskiya,
They themselves report about you what kind of entrance we had to you, and how you turned to God from idols to be slaves to the living and true God,
10 ku kuma jira dawowar Ɗansa daga sama, wanda ya tasa daga matattu, Yesu, wanda ya cece mu daga fushi mai zuwa.
and to wait for His Son coming out of the heavens (whom He raised from among the dead)—Jesus, who preserves us from the coming wrath.

< 1 Tessalonikawa 1 >