< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
Kwakukhona-ke indoda yakoBhenjamini obizo layo linguKishi, indodana kaAbiyeli, indodana kaZerori, indodana kaBekorathi, indodana kaAfiya, umBhenjamini, iqhawe elilamandla.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
Njalo yayilendodana, obizo layo lalinguSawuli, ijaha elihle; kwakungelamuntu omuhle kulalo phakathi kwabantwana bakoIsrayeli; kusukela emahlombe alo kusiya phezulu lalilide kulabo bonke abantu.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
Obabhemikazi bakaKishi, uyise kaSawuli, balahleka-ke. Ngakho uKishi wathi kuSawuli indodana yakhe: Ake uthathe enye yezinceku lawe, usukume uhambe uyedinga obabhemikazi.
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
Wasedabula intaba zakoEfrayimi, wadabula ilizwe leShalisha, kodwa kababatholanga. Basebedabula ilizwe leShalima, kodwa babengekho. Basebedabula ilizwe lakoBhenjamini, kodwa kababatholanga.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
Bona sebefikile elizweni leZufi, uSawuli wathi encekwini yakhe eyayilaye: Woza sibuyele, hlezi ubaba ayekele obabhemikazi abesenqinekela thina.
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
Yasisithi kuye: Khangela-ke, kulomuntu kaNkulunkulu kulumuzi, ungumuntu ohloniphekayo; konke akutshoyo kuyenzeka sibili. Khathesi asiye khona; mhlawumbe angasitshela indlela esizahamba ngayo.
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
USawuli wasesithi encekwini yakhe: Kodwa khangela, uba sisiya, sizamphathelani lowomuntu? Ngoba isinkwa kasisekho ezitsheni zethu; futhi kakulasipho sokusa emuntwini kaNkulunkulu. Silani?
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
Inceku yasibuya yamphendula uSawuli yathi: Khangela, kutholakala esandleni sami ingxenye yesine yeshekeli lesiliva; ngizamnika yona lowomuntu kaNkulunkulu ukuze asitshele indlela yethu.
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
(Endulo koIsrayeli lapho umuntu esiyabuza kuNkulunkulu, wayesitsho kanje: Woza siye kumboni; ngoba lo ongumprofethi lamuhla kuqala wayebizwa ngokuthi ngumboni.)
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
USawuli wasesithi encekwini yakhe: Lihle ilizwi lakho; woza sihambe. Basebesiya emzini lapho okwakukhona lowomuntu kaNkulunkulu.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
Besenyuka ngomqanso womuzi, bona bafica amantombazana ephuma ukuyakukha amanzi, bathi kuwo: Umboni ulapha yini?
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
Asebaphendula athi: Ukhona; khangelani, uphambi kwenu. Phangisani khathesi; ngoba ufike lamuhla emzini, ngoba abantu balomhlatshelo lamuhla endaweni ephakemeyo.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
Ekungeneni kwenu emzini, lizahle limthole engakenyukeli endaweni ephakemeyo ukuyakudla; ngoba abantu kabayikudla aze afike, ngoba nguye obusisa umhlatshelo, emva kwalokho abanxusiweyo badle. Ngakho-ke yenyukani, ngoba yena, phose ngalesisikhathi, lizamthola.
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
Basebesenyukela emzini; besangena phakathi komuzi, khangela, uSamuweli waphuma ukubahlangabeza ukwenyukela endaweni ephakemeyo.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
INkosi yasibonakalisa endlebeni kaSamuweli ngosuku phambi kokufika kukaSawuli, isithi:
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
Kusasa phose ngalesisikhathi ngizathuma kuwe umuntu ovela elizweni lakoBhenjamini; futhi umgcobe abe ngumbusi phezu kwabantu bami uIsrayeli, ukuze asindise abantu bami esandleni samaFilisti, ngoba ngibonile abantu bami, ngoba ukukhala kwabo kufikile kimi.
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
Kwathi uSamuweli ebona uSawuli, iNkosi yamphendula: Khangela, umuntu ebengikhuluma ngaye kuwe. Lo uzabusa phezu kwabantu bami.
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
USawuli wasesondela kuSamuweli phakathi kwesango wathi: Akungitshele, ingaphi lapha indlu yomboni?
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
USamuweli wasemphendula uSawuli wathi: Yimi umboni; yenyuka phambi kwami uye endaweni ephakemeyo, ngoba lamuhla uzakudla lami; lekuseni ngizakuyekela uhambe, ngikutshele konke okusenhliziyweni yakho.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
Lamayelana labobabhemikazi bakho asebelensuku ezintathu belahlekile, ungafaki inhliziyo yakho kubo, ngoba sebetholiwe. Kodwa zikubani iziloyiso zonke zikaIsrayeli? Kazikho kuwe yini lendlini yonke kayihlo?
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
USawuli wasephendula wathi: Kangisuye umBhenjamini yini, owesincinyane sezizwe zakoIsrayeli, losendo lwethu luncinyane kulazo zonke insendo zesizwe sakoBhenjamini? Pho-ke, ukhulumelani kimi ngalindlela?
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
USamuweli wasethatha uSawuli lenceku yakhe, wabangenisa ekamelweni lokudlela, wabahlalisa endaweni engaphezulu yabanxusiweyo, ababengaphose babe ngamatshumi amathathu.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
USamuweli wasesithi kumpheki: Letha isabelo engikunike sona, engithe kuwe ngaso: Sibeke ngakuwe.
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
Umpheki wasephakamisa umlenze lokwakuphezu kwawo, wakubeka phambi kukaSawuli. USamuweli wasesithi: Khangela, okuseleyo; kubeke phambi kwakho, dlana; ngoba bekubekelwe wena kuze kufike lesisikhathi esimisiweyo, njengoba ngitshilo: Nginxuse abantu. USawuli wasesidla loSamuweli ngalolosuku.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
Sebehlile endaweni ephakemeyo baya emzini, wakhuluma loSawuli ephahleni.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
Basebevuka ngovivi; kwasekusithi phose emadabukakusa, uSamuweli wambiza uSawuli ephahleni esithi: Sukuma ukuze ngikuyekele uhambe. Wasesukuma uSawuli, baphuma bobabili, yena loSamuweli, baya phandle.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
Sebesehlela ekucineni komuzi, uSamuweli wathi kuSawuli: Tshela inceku ukuthi yedlule phambi kwethu (yasisedlula), kodwa wena mana okwakhathesi, ukuthi ngikuzwise ilizwi likaNkulunkulu.

< 1 Sama’ila 9 >