< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
Or il y avait un homme de Benjamin, qui avait nom Kis, fort et vaillant; fils d Abiël, fils de Tséror, fils de Becorad, fils d'Aphiah, fils d'un Benjamite;
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
Lequel avait un fils nommé Saül, jeune homme d'élite, et beau, en sorte qu'il n'y avait aucun des enfants d'Israël qui fût plus beau que lui, [et] depuis les épaules en haut il était plus grand qu'aucun du peuple.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
Or les ânesses de Kis, père de Saül s'étaient perdues; et Kis dit à Saül son fils: Prends maintenant avec toi un des serviteurs et te lève, et va chercher les ânesses.
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
Il passa donc par la montagne d'Ephraïm, et traversa le pays de Salisa; mais ils ne les trouvèrent point. Puis ils passèrent par le pays de Sehalim, mais elles n'y furent point; ils passèrent ensuite par le pays de Jémini, mais ils ne les trouvèrent point.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
Quand ils furent venus au pays de Tsuph, Saül dit à son serviteur qui était avec lui: Viens, et retournons-nous-en, de peur que mon père n'ait cessé [d'être en peine] des ânesses, et qu'il ne soit en peine de nous.
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
Et le serviteur lui dit: Voici, je te prie, il y a en cette ville un homme de Dieu, qui est un personnage fort vénérable; tout ce qu'il dit arrive infailliblement; allons y maintenant, peut-être qu'il nous enseignera le chemin que nous devons prendre.
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
Et Saül dit à son serviteur: Mais si nous y allons, que porterons-nous à l'homme de Dieu, car la provision nous a manqué, et nous n'avons aucun présent pour porter à l'homme de Dieu? qu'avons-nous avec nous?
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
Et le serviteur répondit encore à Saül, et dit: Voici j'ai encore entre mes mains le quart d'un sicle d'argent, et je le donnerai à l'homme de Dieu, et il nous enseignera notre chemin.
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
[Or] c'était anciennement [la coutume] en Israël quand on allait consulter Dieu, qu'on se disait l'un à l'autre: Venez, allons au Voyant; car celui qu'on [appelle] aujourd'hui Prophète, s'appelait autrefois le Voyant.
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Et Saül dit à son serviteur: Tu dis bien; viens; allons. Et ils s'en allèrent dans la ville où [était] l'homme de Dieu.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
Et comme ils montaient par la montée de la ville, ils trouvèrent de jeunes filles qui sortaient pour puiser de l'eau, et ils leur dirent: Le Voyant n'est-il pas ici?
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
Et elles leur répondirent, et dirent: Il y est, le voilà devant toi; hâte-toi maintenant, car il est venu aujourd'hui en la ville, parce qu'il y a aujourd'hui un sacrifice pour le peuple dans le haut lieu.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
Comme vous entrerez dans la ville, vous le trouverez avant qu'il monte au haut lieu pour manger; car le peuple ne mangera point jusqu'à ce qu'il soit venu, parce qu'il doit bénir le sacrifice; [et] après cela ceux qui sont conviés [en] mangeront; montez donc maintenant; car vous le trouverez aujourd'hui.
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
Ils montèrent donc à la ville; et comme ils entraient dans la ville, voici, Samuel, qui sortait pour monter au haut lieu, les rencontra.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
Or l'Eternel avait fait entendre et avait dit à Samuel, un jour avant que Saül vînt:
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
Demain à cette même heure je t'enverrai un homme du pays de Benjamin, et tu l'oindras pour être le conducteur de mon peuple d'Israël, et il délivrera mon peuple de la main des Philistins; car j'ai regardé mon peuple, parce que son cri est parvenu jusqu'à moi.
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
Et dès que Samuel eut aperçu Saül, l'Eternel lui dit: Voilà l'homme dont je t'ai parlé; c'est celui qui dominera sur mon peuple.
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
Et Saül s'approcha de Samuel au dedans de la porte, et [lui dit]: Je te prie enseigne-moi où est la maison du Voyant.
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
Et Samuel répondit à Saül, et dit: Je suis le Voyant; monte devant moi au haut lieu, et vous mangerez aujourd'hui avec moi; et je te laisserai aller au matin, et je te déclarerai tout ce que tu as sur le cœur.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
Car quant aux ânesses que tu as perdues il y a aujourd'hui trois jours, ne t'en mets point en peine, parce qu'elles ont été trouvées. Et vers qui [tend] tout le désir d'Israël? n'est ce point vers toi, et vers toute la maison de ton père?
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
Et Saül répondit et dit: Ne suis-je pas Benjamite, de la moindre Tribu d'Israël, et ma famille n'est-elle pas la plus petite de toutes les familles de la Tribu de Benjamin? et pourquoi m'as-tu tenu de tels discours?
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
Samuel donc prit Saül et son serviteur, et les fit entrer dans la salle, et les plaça au plus haut bout, entre les conviés, qui étaient environ trente hommes.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
Et Samuel dit au cuisinier: Apporte la portion que je t'ai donnée, [et] de laquelle je t'ai dit de la serrer par devers toi.
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
Or le cuisinier avait levé une épaule, et ce qui était au dessus, et il la mit devant Saül. Et Samuel dit: Voici ce qui a été réservé, mets-le devant toi, et mange; car il t'a été gardé expressément pour cette heure, lorsque j'ai dit de convier le peuple; et Saül mangea avec Samuel ce jour-là.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
Puis ils descendirent du haut lieu dans la ville, et [Samuel] parla avec Saül sur le toit.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
Puis s'étant levé le matin, à la pointe du jour, Samuel appela Saül sur le toit, et lui dit: Lève-toi, et je te laisserai aller. Saül donc se leva, et ils sortirent eux deux dehors, lui et Samuel.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
Et comme ils descendaient au bas de la ville, Samuel dit à Saül: Dis au serviteur qu'il passe devant nous; lequel passa, mais toi arrête-toi maintenant, afin que je te fasse entendre la parole de Dieu.

< 1 Sama’ila 9 >