< 1 Sama’ila 9 >
1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
Now I there was a man of Benjamin whose name was Cis, the son of Abiel, the son of Seror, the son of Bechorath, the son of Aphia, the son of a man of Jemini, valiant and strong.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
And he had a son whose name was Saul, a choice and goodly man, and there was not among the children of Israel a goodlier person than he: from his shoulders and upward he appeared above all the people.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
And the asses of Cis, Sauls father, were lost: and Cis said to his son Saul: Take one of the servants with thee, and arise, go, and seek the asses. And when they had passed through mount Ephraim,
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
And through the land of Salisa, and had not found them, they passed also through the land of Salim, and they were not there: and through the land of Jemini, and found them not.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
And when they were come to the land of Suph, Saul said to the servant that was with him: Come, let us return, lest perhaps my father forget the asses, and be concerned for us.
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
And he said to him: Behold there is a man of God in this city, a famous man: all that he saith, cometh certainly to pass. Now therefore let us go thither, perhaps he may tell us of our way, for which we are come.
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
And Saul said to his servant: Behold we will go: but what shall we carry to the man of God? the bread is spent in our bags: and we have no present to make to the man of God, nor any thing at all.
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
The servant answered Saul again, and said: Behold there is found in my hand the fourth part of a sicle of silver, let us give it to the man of God, that he may tell us our way.
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
Now in time past, in Israel when a man went to consult God he spoke thus: Come, let us go to the seer. For he that is now called a prophet, in time past was called a seer.
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
And Saul said to his servant: Thy word is very good, come, let us go. And they went into the city, where the man of God was.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
And when they went up the ascent to the city, they found maids coming out to draw water, and they said to them: Is the seer here?
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
They answered and said to them: He is: behold he is before you, make haste now: for he came today into the city, for there is a sacrifice of the people today in the high place.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
As soon as you come into the city, you shall immediately find him, before he go up to the high place to eat: for the people will not eat till he come: because he blesseth the victim, and afterwards they eat that are invited. Now therefore go up, for today you shall find him.
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
And they went up into the city. And when they were walking in the midst of the city, behold Samuel was coming out over against them, to go up to the high place.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
Now the Lord had revealed to the ear of Samuel the day before Saul came, saying:
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
Tomorrow about this same hour I will send thee a man of the land of Benjamin, and thou shalt anoint him to be ruler over my people Israel: and he shall save my people out of the hand of the Philistines: for I have looked down upon my people, because their cry is come to me.
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
And when Samuel saw Saul, the Lord said to him: Behold the man, of whom I spoke to thee, this man shall reign over my people.
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
And Saul came to Samuel in the midst of the gate and said: Tell me, I pray thee, where is the house of the seer?
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
And Samuel answered Saul, saying: I am the seer, go up before me to the high place, that you may eat with me today, and I will let thee go in the morning: and tell thee all that is in thy heart.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
And as for the asses, which were lost three days ago, be not solicitous, because they are found. And for whom shall be all the best things of Israel? Shall they not be for thee and for all thy father’s house?
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
And Saul answering, said: Am not I a son of Jemini of the least tribe of Israel, and my kindred the last among all the families of the tribe of Benjamin? Why then hast thou spoken this word to me?
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
Then Samuel taking Saul and his servant, brought them into the parlour, and gave them a place at the head of them that were invited. For there were about thirty men.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
And Samuel said to the cook: Bring the portion, which I gave thee, and commanded thee to set it apart by thee.
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
And the cook took up the shoulder, and set it before Saul. And Samuel said: Behold what is left, set it before thee, and eat: because it was kept of purpose for thee, when I invited the people. And Saul ate with Samuel that day.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
And they went down from the high place into the town, and he spoke with Saul upon the top of the house: and he prepared a bed for Saul on the top of the house, and he slept.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
And when they were risen in the morning, and it began now to be light, Samuel called Saul on the top of the house, saying: Arise, that I may let thee go. And Saul arose: and they went out both of them, to wit, he and Samuel.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
And as they were going down in the end of the city, Samuel said to Saul: Speak to the servant to go before us, and pass on: but stand thou still a while, that I may tell thee the word of the Lord.