< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
Now there was a man of Benjamin whose name was Kish, the son of Abiel, the son of Zeror, the son of Becorath, the son of Aphiah, the son of a Benjamite, a mighty man of valor.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
And he had a son whose name was Saul, a young man and fine looking. And there was not among the sons of Israel a man better looking than he. From his shoulders and upward he was taller than any of the people.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
And the donkeys of Kish, Saul's father, were lost. And Kish said to Saul his son, Take now one of the servants with thee, and arise, go seek the donkeys.
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
And he passed through the hill-country of Ephraim, and passed through the land of Shalishah, but they did not find them. Then they passed through the land of Shaalim, and they were not there. And he passed through the land of the Benjamites, but they did not find them.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
When they came to the land of Zuph, Saul said to his servant who was with him, Come, and let us return, lest my father leave off caring for the donkeys, and be anxious for us.
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
And he said to him, Behold now, there is in this city a man of God, and he is a man who is held in honor. All that he says comes surely to pass. Now let us go there, perhaps he can tell us concerning our journey on which we go.
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
Then Saul said to his servant, But behold, if we go, what shall we bring the man? For the bread is spent in our vessels, and there is not a present to bring to the man of God. What have we?
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
And the servant answered Saul again, and said, Behold, I have in my hand the fourth part of a shekel of silver. I will give that to the man of God, to tell us our way.
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
(Formerly in Israel, when a man went to inquire of God, thus he said, Come, and let us go to the seer, for he who is now called a Prophet was formerly called a Seer.)
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Then Saul said to his servant, Well said. Come, let us go. So they went to the city where the man of God was.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
As they went up the ascent to the city, they found young maidens going out to draw water, and said to them, Is the seer here?
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
And they answered them, and said, He is. Behold, he is before thee. Make haste now, for he has come today into the city, for the people have a sacrifice today in the high place.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
As soon as ye have come into the city, ye shall straightaway find him before he goes up to the high place to eat. For the people will not eat until he comes, because he blesses the sacrifice, and afterwards those who are bidden eat. Now therefore get you up, for at this time ye shall find him.
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
And they went up to the city. And as they came within the city, behold, Samuel came out toward them, to go up to the high place.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
Now Jehovah had revealed to Samuel a day before Saul came, saying,
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
Tomorrow about this time I will send thee a man out of the land of Benjamin, and thou shall anoint him to be prince over my people Israel. And he shall save my people out of the hand of the Philistines, for I have looked upon my people, because their cry has come to me.
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
And when Samuel saw Saul, Jehovah said to him, Behold, the man of whom I spoke to thee! This man shall have authority over my people.
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
Then Saul drew near to Samuel in the gate, and said, Tell me, I pray thee, where the seer's house is.
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
And Samuel answered Saul, and said, I am the seer. Go up before me to the high place, for ye shall eat with me today. And in the morning I will let thee go, and will tell thee all that is in thy heart.
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
And as for thy donkeys that were lost three days ago, set not thy mind on them, for they are found. And for whom is all that is desirable in Israel? Is it not for thee, and for all thy father's house?
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
And Saul answered and said, Am I not a Benjamite, of the smallest of the tribes of Israel? And my family the least of all the families of the tribe of Benjamin? Why then speak thou to me according to this manner?
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
And Samuel took Saul and his servant, and brought them into the guest-chamber, and made them sit in the chief place among those who were bidden, who were about thirty men.
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
And Samuel said to the cook, Bring the portion which I gave thee, of which I said to thee, Set it by thee.
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
And the cook took up the thigh, and that which was upon it, and set it before Saul. And Samuel said, Behold, that which has been reserved! Set it before thee and eat, because it has been kept for thee to the appointed time, for I said, I have invited the people. So Saul ate with Samuel that day.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
And when they came down from the high place into the city, he conversed with Saul upon the housetop.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
And they arose early. And it came to pass about the dawning of the day, that Samuel called to Saul on the housetop, saying, Up, that I may send thee away. And Saul arose, and they went out both of them, he and Samuel, abroad.
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
As they were going down at the end of the city, Samuel said to Saul, Bid the servant pass on before us (and he passed on), but stand thou still first, that I may cause thee to hear the word of God.

< 1 Sama’ila 9 >