< 1 Sama’ila 9 >

1 An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
I Benjamin var der en Mand ved Navn Kisj, en Søn af Abiel, en Søn af Zeror, en Søn af Bekorat, en Søn af Afia, en Benjaminit, en formuende Mand.
2 Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
Han havde en Søn ved Navn Saul, statelig og smuk, ingen blandt Israeliterne var smukkere end han; han var et Hoved højere end alt Folket.
3 To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
Engang var nogle af Sauls Fader Kisj's Æsler blevet borte, og Kisj sagde da til sin Søn Saul: »Tag en af Karlene med og gaa ud og søg efter Æslerne!«
4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
De gik saa først gennem Efraims Bjerge og Sjalisjaegnen, men fandt dem ikke; derefter gik de gennem Sja'alimegnen, men der var de heller ikke; derpaa gik de gennem Benjamins Land, men fandt dem ikke.
5 Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
Da de kom til Zufegnen, sagde Saul til Karlen, som var med ham: »Kom, lad os vende hjem, for at min Fader ikke skal holde op med at tænke paa Æslerne og i Stedet blive urolig for os!«
6 Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
Men han svarede ham: »Se, i Byen der bor en Guds Mand, en anset Mand; hvad han siger, sker altid. Lad os nu gaa derhen, maaske kan han give os Besked angaaende det, vi gaar om.«
7 Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
Da sagde Saul til Karlen: »Ja, lad os gaa derhen! Men hvad skal vi give Manden? Thi vi har ikke mere Brød i vore Tasker, og nogen Gave har vi ikke at give den Guds Mand. Hvad har vi?«
8 Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
Karlen svarede atter Saul: »Se, jeg har en kvart Sekel Sølv, den kan du give den Guds Mand; saa siger han os nok Besked om det, vi gaar om.«
9 (A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
Fordum sagde man i Israel, naar man gik hen for at raadspørge Gud: »Kom, lad os gaa til Seeren!« Thi hvad man nu til Dags kalder en Profet, kaldte man fordum en Seer.
10 Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
Da sagde Saul til Karlen: »Du har Ret! Kom, lad os gaa derhen!« Saa gik de hen til Byen, hvor den Guds Mand boede.
11 Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
Som de nu gik ad Vejen op til Byen, traf de nogle unge Piger, der gik ud for at øse Vand, og de spurgte dem: »Er Seeren her?«
12 ’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
De svarede dem: »Ja, han er foran; han kom til Byen lige nu. Folket ofrer nemlig i Dag et Slagtoffer paa Offerhøjen.
13 Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
Naar I blot gaar ind i Byen, kan I træffe ham, før han gaar op paa Offerhøjen til Maaltidet; thi Folket spiser ikke, før han kommer, da han skal velsigne Slagtofferet; saa først spiser de indbudne. Gaa nu op til Byen, thi netop nu kan I træffe ham!«
14 Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
De gik saa op til Byen; og som de gik ind igennem Porten, kom Samuel gaaende imod dem paa Vej op til Offerhøjen.
15 Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
HERREN havde Dagen før Sauls Komme aabnet Samuels Øre og sagt:
16 “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
»I Morgen ved denne Tid sender jeg en Mand til dig fra Benjamins Land; ham skal du salve til Fyrste over mit Folk Israel; han skal frelse mit Folk fra Filisternes Haand; thi jeg har givet Agt paa mit Folks Nød, dets Klageraab har naaet mig!«
17 Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
Og straks da Samuel fik Øje paa Saul, sagde HERREN til ham: »Se, der er den Mand, om hvem jeg sagde til dig: Han skal herske over mit Folk!«
18 Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
Da traadte Saul hen til Samuel midt i Porten og sagde: »Vær saa god at sige mig, hvor Seerens Hus er!«
19 Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
Samuel svarede: »Seeren — det er mig; gaa i Forvejen op paa Offerhøjen; du skal spise sammen med mig i Dag; i Morgen skal jeg følge dig paa Vej og kundgøre dig alt, hvad der er i dit Hjerte;
20 Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
for Æslerne, som for tre Dage siden blev borte for dig, skal du ikke ængste dig; de et fundet. Men til hvem staar alt Israels Begær uden til dig og hele dit Fædrenehus?«
21 Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
Da svarede Saul: »Er jeg ikke fra Benjamin, Israels mindste Stamme? Og min Slægt er den ringeste af alle Benjamins Stammes Slægter. Hvor kan du da tale saaledes til mig?«
22 Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
Men Samuel tog Saul og hans Karl, førte dem til Gildesalen og gav dem Plads øverst blandt de indbudne — der var omtrent tredive Mænd —
23 Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
og Samuel sagde til Kokken: »Ræk mig det Stykke, jeg gav dig og sagde, du skulde lægge til Side!«
24 Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
Da tog Kokken Køllen og satte den for Saul. Og Samuel sagde: »Se, Kødet staar for dig, spis! Thi til den fastsatte Tid har man ventet dig, for at du kunde spise sammen med de indbudne.« Saa spiste Saul sammen med Samuel den Dag.
25 Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
Derpaa steg de ned fra Offerhøjen til Byen, og der blev redt til Saul paa Taget.
26 Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
Saa lagde han sig til Hvile. Tidligt om Morgenen, da Morgenrøden brød frem, raabte Samuel til Saul oppe paa Taget: »Staa op, jeg vil følge dig paa Vej!« Da stod Saul op, og han og Samuel gik ud sammen,
27 Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”
Men da de paa Nedvejen var kommet til Udkanten af Byen, sagde Samuel til Saul: »Sig til Karlen, at han skal gaa i Forvejen! Men bliv du staaende et Øjeblik, saa vil jeg kundgøre dig Guds Ord!«

< 1 Sama’ila 9 >