< 1 Sama’ila 8 >
1 Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
Pripetilo se je, ko je bil Samuel star, da je svoja sinova postavil za sodnika nad Izraelom.
2 Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
Torej ime njegovega prvorojenca je bilo Joél in ime njegovega drugega Abíja. Bila sta sodnika v Beeršébi.
3 Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
Njegova sinova pa nista hodila po njegovih poteh, temveč sta se obrnila stran za dobičkom in jemala podkupnine in izkrivljala sodbo.
4 Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
Potem so se vse starešine Izraela zbrali skupaj in prišli k Samuelu v Ramo
5 Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
in mu rekli: »Glej, star si in tvoja sinova ne hodita po tvojih poteh. Sedaj nam postavi kralja, da nas sodi, kakor [imajo] vsi narodi.«
6 Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
Toda stvar je razžalila Samuela, ko so rekli: »Daj nam kralja, da nas sodi.« Samuel je molil h Gospodu.
7 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
Gospod je rekel Samuelu: »Prisluhni glasu ljudstva v vsem, kar ti rečejo, kajti niso zavrnili tebe, temveč so zavrnili mene, da ne bi kraljeval nad njimi.
8 Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
Glede na vsa dela, ki so jih storili od dne, ko sem jih privedel gor iz Egipta, celo do tega dne, s čimer so zapustili mene in služili drugim bogovom, tako delajo tudi tebi.
9 Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
Zdaj torej prisluhni njihovemu glasu, vendar jih slovesno posvari in jim pokaži navade kralja, ki bo kraljeval nad njimi.«
10 Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
Samuel je ljudstvu, ki je od njega zahtevalo kralja, povedal vse Gospodove besede.
11 Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
Rekel je: »To bo navada kralja, ki bo kraljeval nad vami: ›Vzel bo vaše sinove in jih določil zase, za svoje bojne vozove in da bodo njegovi konjeniki in nekateri bodo tekli pred njegovimi bojnimi vozovi.
12 Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
Določil si bo tisočnike in poveljnike nad petdesetimi in postavil jih bo, da orjejo njegovo zemljo, da žanjejo njegovo žetev, da izdelajo njegova bojna orodja in orodja njegovih bojnih vozov.
13 Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
Vzel bo vaše hčere, da bodo izdelovalke dišečin in da bodo kuharice in pekarice.
14 Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
Vzel bo vaša polja in vaše vinograde in vaše oljčne nasade, celó najboljše izmed njih in jih dal svojim služabnikom.
15 Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
Vzel bo desetino od vašega semena in od vaših vinogradov in dal svojim častnikom in svojim služabnikom.
16 Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
Vzel bo vaše služabnike, vaše dekle, vaše najčednejše mladeniče, vaše osle in jih postavil k svojemu delu.
17 Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
Vzel bo desetino od vaših ovc in vi boste njegovi služabniki.
18 Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
Vpili boste na ta dan zaradi svojega kralja, ki si ga boste izbrali, Gospod pa vas na ta dan ne bo slišal.‹«
19 Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
Kljub temu je ljudstvo odklonilo, da uboga Samuelov glas in rekli so: »Ne, temveč bomo imeli kralja nad seboj,
20 Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
da bomo tudi mi lahko podobni vsem narodom in da nam bo naš kralj lahko sodil in bo pred nami šel ven in bojeval naše boje.«
21 Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
Samuel je slišal vse besede ljudstva in jih ponovil v Gospodova ušesa.
22 Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”
Gospod je Samuelu rekel: »Prisluhni njihovemu glasu in postavi jim kralja.« Samuel je rekel Izraelovim možem: »Pojdite vsak mož v svoje mesto.«