< 1 Sama’ila 8 >

1 Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
Kwasekusithi uSamuweli esemdala wabeka amadodana akhe ukuze abe ngabahluleli koIsrayeli.
2 Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
Lebizo lendodana yakhe elizibulo lalinguJoweli, lebizo leyesibili yakhe linguAbhiya; ayengabahluleli eBherishebha.
3 Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
Kodwa amadodana akhe ayengahambi ngendlela zakhe, kodwa aphambukela enzuzweni embi, emukela isivalamlomo, aphambula isahlulelo.
4 Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
Kwasekubuthana abadala bonke bakoIsrayeli, beza kuSamuweli eRama,
5 Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
bathi kuye: Khangela, wena usumdala, lamadodana akho kawahambi ngendlela zakho; ngakho sibekele inkosi ukuze isahlulele njengazo zonke izizwe.
6 Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
Kodwa leyonto yayimbi emehlweni kaSamuweli lapho besithi: Sinike inkosi ukusahlulela. USamuweli wasekhuleka eNkosini.
7 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
INkosi yasisithi kuSamuweli: Lalela ilizwi labantu kukho konke abakutshoyo kuwe, ngoba kakusuwe abakwalayo, kodwa bala mina ukuze ngingabusi phezu kwabo.
8 Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
Ngokwezenzo zonke abazenzileyo kusukela ngosuku engabenyusa ngalo eGibhithe kuze kube lamuhla, bangitshiyile bakhonza abanye onkulunkulu; benza njalo lakuwe.
9 Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
Ngakho khathesi, lalela ilizwi labo; kodwa nxa ubafakazele kakhulu, ubazise indlela yenkosi ezabusa phezu kwabo.
10 Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
USamuweli wasetshela abantu abacela kuye inkosi wonke amazwi eNkosi.
11 Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
Wasesithi: Le izakuba yindlela yenkosi ezabusa phezu kwenu; izathatha amadodana enu izibekele wona enqoleni zayo lakubagadi bamabhiza ayo, agijime phambi kwezinqola zayo.
12 Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
Izazibekela wona abe yizinduna zezinkulungwane lezinduna zamatshumi amahlanu, lokulima amasimu ayo, lokuvuna isivuno sayo, lokwenza izikhali zayo zempi, lezikhali zezinqola zayo.
13 Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
Izathatha amadodakazi enu iwenze abe ngabenzi bamakha, labapheki, labaphekizinkwa.
14 Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
Izathatha amasimu enu, lezivini zenu lezivande zenu zemihlwathi, ezinhle, ikunike inceku zayo.
15 Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
Izathatha okwetshumi yenhlanyelo yenu leyezivini zenu, iyinike induna zayo lenceku zayo.
16 Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
Izathatha inceku zenu lencekukazi zenu lamajaha enu angcono labobabhemi benu, ikusebenzise emsebenzini wayo.
17 Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
Izathatha okwetshumi kwemihlambi yenu; lina-ke libe yizinceku zayo.
18 Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
Njalo lizakhala ngalolosuku ngenxa yenkosi yenu elizikhethele yona; kodwa iNkosi kayiyikuliphendula mhlalokho.
19 Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
Kodwa abantu bala ukulilalela ilizwi likaSamuweli, bathi: Hatshi, kodwa kuzakuba lenkosi phezu kwethu,
20 Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
ukuze lathi sibe njengezizwe zonke, lenkosi yethu isahlulele, iphume phambi kwethu, ilwe izimpi zethu.
21 Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
USamuweli esewazwile wonke amazwi abantu, wawalandisa endlebeni zeNkosi.
22 Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”
INkosi yasisithi kuSamuweli: Lalela ilizwi labo, ubabekele inkosi. USamuweli wasesithi emadodeni akoIsrayeli: Hambani liye ngulowo lalowo emzini wakhe.

< 1 Sama’ila 8 >