< 1 Sama’ila 8 >

1 Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
Et Samuel devint vieux, et il institua ses fils juges d'Israël.
2 Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
Voici les noms de ces fils: le premier-né s'appelait Joël, le second Abia; ils jugeaient en Bersabée.
3 Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
Mais ses fils ne marchèrent pas en ses voies; ils en furent détournés par l'intérêt; ils acceptèrent des présents et ils firent dévier la justice.
4 Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
En conséquence, les fils d'Israël se rassemblèrent; ils allèrent trouver Samuel en Armathem,
5 Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
Et ils lui dirent: Écoute, tu es devenu vieux, et tes fils ne marchent pas en tes voies; donne-nous donc un roi comme en ont les autres nations, afin qu'il nous juge.
6 Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
Cette parole parut mauvaise à Samuel, lorsqu'ils dirent: Donne-nous un roi, afin qu'il nous juge; et Samuel pria le Seigneur.
7 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
Or, le Seigneur dit à Samuel: Écoute la voix du peuple, fais comme ils te diront; ce n'est point toi, c'est moi qu'ils ont méprisé et dont ils ne veulent pas pour régner sur eux.
8 Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
C'est ce qu'ils ont toujours fait à mon égard depuis le jour où je les ai tirés de l'Égypte jusqu'à ce moment: ils m'ont abandonné, et ils ont servi d'autres dieux; ils te traitent de même maintenant.
9 Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
Obéis donc à leur voix; seulement prends-les à témoin, et prends-les à témoin pour leur faire connaître les droits du roi qui règnera sur eux.
10 Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
Et Samuel répéta toutes les paroles du Seigneur au peuple qui lui demandait un roi.
11 Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
Il leur dit: Voici quels seront les droits du roi qui régnera sur vous: Il prendra vos fils, et il les placera sur ses chars de guerre ou parmi ses cavaliers; il les fera courir devant ses chars.
12 Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
Il s'en fera des centeniers et des chefs de mille hommes; il leur fera faire sa moisson et sa vendange; il leur fera fabriquer des armes de guerre, et les pièces diverses de ses chariots.
13 Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
Il prendra vos filles pour préparer ses parfums, cuire son pain, et faire sa cuisine.
14 Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
Il prendra vos champs, vos vignes, vos meilleurs oliviers, pour les donner à ses serviteurs.
15 Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
Il prendra la dîme de vos grains et de votre vendange, pour la donner à ses eunuques et à ses esclaves.
16 Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
Il prendra vos serviteurs, vos servantes, vos bœufs et vos ânes; il prendra la dîme de tous les fruits de vos travaux.
17 Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
Il prendra la dîme de votre bétail, et vous serez ses esclaves.
18 Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
Et, ce jour-là, vous crierez à cause du roi que vous vous serez choisi; et, ce jour-là, le Seigneur ne vous écoutera point, parce que c'est vous-mêmes qui aurez voulu ce roi pour vous.
19 Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
Mais le peuple ne voulut pas écouter Samuel, et il dit: Nullement, mais nous aurons un roi,
20 Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
Nous serons comme toutes les nations; notre roi nous jugera, il marchera à notre tête et il dirigera nos guerres.
21 Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
Et Samuel écouta tous les discours du peuple, et il les transmit au Seigneur.
22 Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”
Et le Seigneur dit à Samuel: Obéis-leur, et donne-leur un roi. Alors, Samuel dit aux fils d'Israël: Que chacun s'en retourne en sa ville.

< 1 Sama’ila 8 >