< 1 Sama’ila 8 >
1 Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
When Samuel was nowe become olde, he made his sonnes Iudges ouer Israel.
2 Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
(And the name of his eldest sonne was Ioel, and the name of the second Abiah) euen Iudges in Beer-sheba.
3 Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
And his sonnes walked not in his wayes, but turned aside after lucre, and tooke rewards, and peruerted the iudgement.
4 Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
Wherefore all the Elders of Israel gathered them together, and came to Samuel vnto Ramah,
5 Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
And said vnto him, Beholde, thou art olde, and thy sonnes walke not in thy wayes: make vs nowe a King to iudge vs like all nations.
6 Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
But the thing displeased Samuel, when they said, Giue vs a King to iudge vs: and Samuel prayed vnto the Lord.
7 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
And the Lord said vnto Samuel, Heare the voyce of the people in all that they shall say vnto thee: for they haue not cast thee away, but they haue cast me away, that I should not reigne ouer the.
8 Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
As they haue euer done since I brought them out of Egypt euen vnto this day, (and haue forsaken me, and serued other gods) euen so doe they vnto thee.
9 Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
Nowe therefore hearken vnto their voyce: howbeit yet testifie vnto them, and shewe them the maner of ye King that shall reigne ouer them.
10 Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
So Samuel told all the wordes of the Lord vnto the people that asked a King of him.
11 Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
And he saide, This shall be the maner of the King that shall reigne ouer you: he will take your sonnes, and appoint them to his charets, and to be his horsemen, and some shall runne before his charet.
12 Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
Also he will make them his captaines ouer thousands, and captaines ouer fifties, and to eare his ground, and to reape his haruest, and to make instruments of warre, and the thinges that serue for his charets.
13 Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
He will also take your daughters and make them apoticaries, and cookes, and bakers.
14 Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
And he will take your fieldes, and your vineyardes, and your best Oliue trees, and giue them to his seruants.
15 Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
And he will take the tenth of your seede, and of your vineyards, and giue it to his Eunuches, and to his seruants.
16 Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
And he will take your men seruants, and your maide seruants, and the chiefe of your yong men, and your asses, and put them to his worke.
17 Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
He will take the tenth of your sheepe, and ye shall be his seruants.
18 Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
And ye shall crie out at that day, because of your King, whom ye haue chosen you, and the Lord will not heare you at that day.
19 Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
But the people would not heare the voyce of Samuel, but did say, Nay, but there shall be a King ouer vs.
20 Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
And we also will be like all other nations, and our King shall iudge vs, and goe out before vs, and fight our battels.
21 Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
Therefore when Samuel heard all ye wordes of ye people, he rehearsed the in ye eares of ye Lord.
22 Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”
And the Lord saide to Samuel, Hearken vnto their voyce, and make them a King. And Samuel said vnto the men of Israel, Goe euery man vnto his citie.