< 1 Sama’ila 7 >

1 Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
Les gens de Kiryath-Yearim vinrent prendre l’arche du Seigneur, la transportèrent dans la maison d’Abinadab, sur la colline, et consacrèrent son fils Eléazar pour lui en confier la garde.
2 Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
Or, depuis que l’arche résidait à Kiryath-Yearim, il s’était écoulé bien des jours, vingt années déjà, lorsque toute la maison d’Israël aspira à revenir vers l’Eternel.
3 Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
Alors Samuel parla ainsi à toute la maison d’Israël: "Si c’est de tout votre cœur que vous retournez à l’Eternel, écartez du milieu de vous les dieux étrangers et les Astaroth; dirigez votre cœur vers l’Eternel, ne servez que lui seul, et il vous sauvera de la main des Philistins."
4 Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
Les Israélites firent disparaître les Bealim et les Astaroth, et servirent uniquement l’Eternel.
5 Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
Et Samuel dit: "Faites assembler tout Israël à Miçpa, que je prie l’Eternel en votre faveur."
6 Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
Ils s’assemblèrent à Miçpa; là on puisa de l’eau, qu’on répandit devant le Seigneur, et l’on jeûna en ce jour en disant: "Nous avons péché devant l’Eternel!" Et Samuel exerça le pouvoir sur les enfants d’Israël à Miçpa.
7 Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
Or, les Philistins ayant appris que les Israélites s’étaient réunis à Miçpa, leurs princes marchèrent contre Israël; les Israélites en furent informés, et ils eurent peur des Philistins.
8 Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
Et ils dirent à Samuel: "Ne nous refuse pas d’implorer l’Eternel, notre Dieu, pour qu’il nous sauve de la main des Philistins!"
9 Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
Samuel prit un agneau de lait, qu’il offrit tout entier en holocauste au Seigneur; puis il implora le Seigneur pour Israël, et le Seigneur l’exauça.
10 Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
Tandis que Samuel offrait l’holocauste, les Philistins s’avancèrent pour attaquer Israël; mais le Seigneur tonna en ce moment, avec grand fracas, sur les Philistins, les étourdit, et ils furent battus par Israël.
11 Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
Les gens d’Israël s’élancèrent de Miçpa à la poursuite des Philistins, et les battirent jusque sous Beth-Car.
12 Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
Samuel prit alors une pierre, qu’il posa entre Miçpa et Chên et qu’il appela Eben-Haézer, en disant: "Dieu nous a assistés jusqu’ici."
13 Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
Ainsi les Philistins furent matés, et ne tentèrent plus de pénétrer sur le territoire d’Israël; car la main de l’Eternel pesa sur eux tant que vécut Samuel.
14 Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
Les villes que les Philistins avaient prises à Israël furent recouvrées par lui, depuis Ekron jusqu’à Gath, ainsi que leur territoire, qu’Israël reprit sur les Philistins. Il y avait paix, d’ailleurs, entre Israël et les Amorréens.
15 Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
Samuel conserva le gouvernement d’Israël sa vie durant.
16 Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
Tous les ans il faisait un voyage, parcourant Béthel, Ghilgal, Miçpa, et rendait la justice à Israël dans toutes ces villes;
17 Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.
puis il revenait à Rama, car là était sa maison, et c’est là qu’il gouvernait Israël. Il y éleva aussi un autel au Seigneur.

< 1 Sama’ila 7 >