< 1 Sama’ila 7 >

1 Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
And the men of Kiryath-ye'arim came, and fetched up the ark of the Lord, and brought it unto the house of Abinadab on the hill, and Elazar his son they sanctified to guard the ark of the Lord.
2 Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
And it came to pass, from the time the ark remained in Kiryath-ye'arim, and the time was long, and it was twenty years: that all the house of Israel followed anxiously after the Lord.
3 Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
And Samuel said unto all the house of Israel, as followeth, If with all your heart ye do return unto the Lord, then put away the gods of the stranger and the 'Ashtaroth from your midst, and direct your heart unto the Lord, and serve him alone: and then will he deliver you out of the hand of the Philistines.
4 Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
Then did the children of Israel put away the Be'alim and the 'Ashtaroth, and served the Lord alone.
5 Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
And Samuel said, Assemble all Israel together at Mizpah, and I will pray in your behalf unto the Lord.
6 Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
And they assembled themselves together at Mizpah, and drew water, and poured it out before the Lord, and fasted on that day, and said there, We have sinned against the Lord. And Samuel judged the children of Israel in Mizpah.
7 Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
And when the Philistines heard that the children of Israel had assembled themselves at Mizpah, the lords of the Philistines went up against Israel. And when the children of Israel heard it, they were afraid of the Philistines.
8 Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
And the children of Israel said to Samuel, Do not abstain, so as not to cry for us unto the Lord our God, that he may help us out of the hand of the Philistines.
9 Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
And Samuel took one sucking lamb, and offered it for an entire burnt-offering unto the Lord: and Samuel cried unto the Lord in behalf of Israel; and the Lord answered him.
10 Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
And as Samuel was offering up the burnt-offering, the Philistines drew near to battle against Israel; but the Lord thundered with a loud noise on that day over the Philistines, and brought them into confusion, and they were smitten before Israel.
11 Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
And the men of Israel went out of Mizpah, and pursued the Philistines, and smote them, as far as below Beth-car.
12 Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
And Samuel took one stone, and set it between Mizpah and Shen, and called its name Eben-ha'ezer, saying, As far as this hath the Lord helped us.
13 Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
So were the Philistines humbled, and they came no more into the territory of Israel; and the hand of the Lord was against the Philistines all the days of Samuel.
14 Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
And the cities which the Philistines had taken from Israel came again to Israel, from 'Ekron even unto Gath, and their territory did Israel deliver out of the hand of the Philistines. And there was peace between Israel and the Emorites.
15 Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
And Samuel judged Israel all the days of his life.
16 Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
And he went from year to year and traveled in circuit to Beth-el, and Gilgal, and Mizpah, and judged Israel in all these places.
17 Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.
And his return was to Ramah; for there was his house; and there he judged Israel: and he built there an altar unto the Lord.

< 1 Sama’ila 7 >