< 1 Sama’ila 7 >

1 Mutanen Kiriyat Yeyarim suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji. Suka kai a gidan Abinadab da ke kan tudu, suka keɓe Eleyazar ɗansa yă lura da akwatin alkawarin Ubangiji.
Then the men of Kiriath-jearim arrived, and they led away the ark of the Lord. And they brought it into the house of Abinadab, in Gibeah. Then they sanctified Eleazar, his son, so that he might care for the ark of the Lord.
2 Akwatin Alkawarin ya daɗe a Kiriyat Yeyarim ya kai shekara ashirin cif. Sai dukan mutanen Isra’ila suka yi makoki suka nemi Ubangiji.
And it happened that, from that day, the ark of the Lord remained in Kiriath-jearim. And the days were multiplied (for it was now the twentieth year) and all the house of Israel rested, following the Lord.
3 Saboda haka Sama’ila ya yi magana da dukan gidan Isra’ila ya ce, in har da zuciya ɗaya kuke juyowa ga Ubangiji sai ku raba kanku da baƙin alloli da gunkin nan Ashtarot, ku ba da kanku ga Ubangiji. Ku yi masa bauta shi kaɗai, zai kuɓutar da ku daga hannun Filistiyawa.
Then Samuel spoke to the entire house of Israel, saying: “If you would return to the Lord with your whole heart, take away strange gods from among you, the Baals and Ashtaroth, and prepare your hearts for the Lord, and serve him alone. And he will rescue you from the hand of the Philistines.”
4 Sai Isra’ilawa suka rabu da gumakan Ba’al da Ashtarot suka bauta wa Ubangiji kaɗai.
Therefore, the sons of Israel took away the Baals and Ashtaroth, and they served the Lord alone.
5 Sama’ila ya ce, “Ku tattara dukan Isra’ila a Mizfa, ni kuwa zan yi addu’a ga Ubangiji dominku.”
And Samuel said, “Gather all of Israel at Mizpah, so that I may pray for you to the Lord.”
6 Sa’ad da suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa suka zuba a gaban Ubangiji. A wannan rana suka yi azumi suka tuba, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi!” Sama’ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra’ilawa.
And they convened at Mizpah. And they drew water, and they poured it out in the sight of the Lord. And on that day they fasted, and in that place they said, “We have sinned against the Lord.” And Samuel judged the sons of Israel at Mizpah.
7 Da Filistiyawa suka ji cewa Isra’ila sun taru a Mizfa, sai shugabanninsu suka zo don su yaƙe Isra’ila. Da Isra’ilawa suka ji labarin, sai suka tsorata saboda Filistiyawa.
And the Philistines heard that the sons of Israel had gathered together at Mizpah. And the princes of the Philistines ascended against Israel. And when the sons of Israel had heard this, they were afraid before the face of the Philistines.
8 Suka ce wa Sama’ila, “Kada ka fasa kai kukanmu ga Ubangiji Allahnmu saboda mu, don yă cece mu daga hannun Filistiyawa.”
And they said to Samuel, “May you not cease to cry out to the Lord our God on our behalf, so that he may save us from the hand of the Philistines.”
9 Sama’ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya yi roƙo ga Ubangiji a madadin Isra’ila, Ubangiji kuwa ya amsa addu’arsa.
Then Samuel took one suckling lamb, and he offered it whole, as a holocaust to the Lord. And Samuel cried out to the Lord on behalf of Israel, and the Lord heeded him.
10 Lokacin da Sama’ila yana miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso kusa don su yi yaƙi da Isra’ila. A ranar Ubangiji ya sa babban tsawa ya ruɗar da Filistiyawa har suka gudu a gaban Isra’ilawa.
Then it happened that, while Samuel was offering the holocaust, the Philistines began the battle against Israel. But the Lord thundered with a great crash, on that day, over the Philistines, and he terrified them, and they were cut down before the face of Israel.
11 Isra’ilawa suka fito a guje daga Mizfa suka fafari Filistiyawa suka yi ta karkashe su a hanya har kwarin Bet-Kar.
And the men of Israel, departing from Mizpah, pursued the Philistines, and they struck them down as far as the place which was below Bethcar.
12 Sa’an nan Sama’ila ya ɗauki dutse ya kafa tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer ma’ana, “Har zuwa wannan lokaci Ubangiji ya taimake mu.”
Then Samuel took a single stone, and he placed it between Mizpah and Shen. And he called the name of this place: The Stone of Assistance. And he said, “For in this place the Lord gave assistance to us.”
13 Ta haka Isra’ilawa suka ci Filistiyawa. Daga ranan Filistiyawa ba su ƙara yin nasara a kan Isra’ila ba. Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa har ƙarshen zamanin Sama’ila.
And the Philistines were humbled, and they no longer drew near, so that they might enter into the borders of Israel. And so, the hand of the Lord was over the Philistines during all the days of Samuel.
14 Filistiyawa suka mayar wa Isra’ila da garuruwan da suka ƙwato, wato, daga Ekron zuwa Gat, dukan yankin ƙasarsu da yake ƙarƙashin ikon Filistiyawa. Aka kuma sami zaman lafiya tsakanin Isra’ilawa da Amoriyawa.
And the cities that the Philistines had taken from Israel were restored to Israel, from Ekron as far as Gath, with their borders. And he freed Israel from the hand of the Philistines. And there was peace between Israel and the Amorites.
15 Sama’ila kuwa ya ci gaba da mulkin Isra’ila dukan rayuwarsa.
And Samuel judged Israel all the days of his life.
16 Shekara-shekara Sama’ila yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal da Mizfa inda yakan yi musu shari’a.
And he went each year, traveling around to Bethel, and to Gilgal, and to Mizpah, and he judged Israel in the above-stated places.
17 Amma yakan komo Rama inda gidansa yake, a nan yakan yi wa Isra’ila shari’a. A nan ne kuma ya gina wa Ubangiji bagade.
And he returned to Ramah. For his house was there, and he judged Israel there. And then he built an altar to the Lord there.

< 1 Sama’ila 7 >