< 1 Sama’ila 6 >
1 Lokacin da akwatin alkawarin Ubangiji ya kai wata bakwai a ƙasar Filistiyawa.
L'arche fut sept mois sur la terre des étrangers, et les rats y fourmillèrent.
2 Filistiyawa suka kira firistoci da bokaye suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku gaya mana yadda za mu komar da shi inda ya fito.”
Alors, les Philistins appelèrent leurs prêtres, leurs devins, leurs magiciens, et ils leur dirent: Que ferons-nous de l'arche du Seigneur? Apprenez-nous comment nous la renverrons au lieu où elle réside.
3 Suka ce, in za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra’ila kada ku komar da shi hannu wofi; amma ku tabbata kun aika da hadaya don laifi zuwa wurinsa. Sa’an nan za ku warke ku kuma san dalilin da ya sa bai cire hannunsa a kanku ba.
Et ils dirent: Si vous renvoyez l'arche de l'alliance du Seigneur Dieu d'Israël, ne la renvoyez point vide; mais en la rendant faites des dons à cause de votre plaie; cela fait, vous serez guéris, l'arche vous sera propice, et la main du Seigneur ne pèsera plus sur vous.
4 Filistiyawa suka ce, “Wace irin hadaya don laifi za mu aika masa?” Suka ce, “Marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa. Saboda annoba iri ɗaya ce ta buga ku da shugabanninku.
Que donnerons-nous à cause de notre plaie? dirent-ils; les prêtres répondirent:
5 Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye da suke hallaka gari, ku ba da girma ga Allah na Isra’ila. Wataƙila zai ɗauke hukuncinsa daga gare ku da allolinku da kuma ƙasarku.
Et autant de rats d'or semblables aux rats qui ont dévasté votre contrée. Vous glorifierez ainsi le Seigneur afin que sa main cesse de peser sur vous, sur vos dieux et sur votre pays.
6 Me ya sa kun taurare kanku kamar yadda Masarawa da Fir’auna suka yi? Da ya ba su matsanancin wahala, ba su bar Isra’ilawa suka tafi hanyarsu ba?
Pourquoi vous endurcir le cœur, comme l'ont endurci l'Égypte et le Pharaon? N'est-ce pas après que le Seigneur se fut joué d'eux, qu'ils congédièrent les Hébreux et que ceux-ci partirent.
7 “Yanzu fa ku shirya sabon keken shanu da shanu biyu masu ba wa’ya’yansu nono, waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba. Ku daure keken shanu wa shanun, amma ku tsare’yan maruƙansu a gida.
Maintenant donc prenez du bois et faites un chariot neuf; prenez deux vaches n'ayant vêlé qu'une fois, séparez-les de leurs veaux; attelez-les au chariot, et renvoyez les veaux à l'étable.
8 Ku ɗauki wani akwati ku sa siffofin zinariyan nan a ciki, waɗanda za su zama kyautai na shafen laifi, ku ajiye kusa da Akwati na UBANGIJI. Bayan haka sai ku sa keken shanun da akwatin a hanya, ku bar shi yă tafi.
Ensuite, vous prendrez l'arche et vous la placerez sur le chariot avec tous les objets d'or que vous donnerez en expiation, et que vous renfermerez dans une cassette à côté d'elle; puis, vous la renverrez, vous pousserez l'attelage et vous vous en éloignerez.
9 Amma ku zuba ido ku ga in ya haura zuwa yankinsa, zuwa Bet-Shemesh, to, Ubangiji ne ya kawo mana babban masifar a kanmu. Amma in bai bi ta nan ba, za mu san cewa ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.”
Après cela, vous serez attentifs: si elle prend par Bethsamys la route de son pays, c'est le Seigneur qui vous a frappés de ces grandes plaies; sinon, nous reconnaîtrons que ce n'est point sa main qui nous a touchés, mais qu'un accident nous est advenu.
10 Suka yi haka. Suka ɗauki shanun tatsa guda biyu suka ɗaura musu keken shanu, suka tsare’yan maruƙansu a gida.
Les Philistins suivirent ces conseils; ils prirent deux vaches qui n'avaient encore vêlé qu'une fois; ils les attelèrent au chariot, et ils retinrent leurs veaux à l'étable.
11 Suka aza akwatin alkawarin Ubangiji a bisa keken shanun tare da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran.
ils posèrent sur le chariot l'arche du Seigneur et la cassette contenant les rats d'or.
12 Sai shanun suka miƙe zuwa Bet-Shemesh. Suka bi hanya daidai, ba su juya dama ko hagu ba. Shugabannin Filistiyawa suka bi har zuwa iyakar ƙasar Bet-Shemesh.
Et les vaches marchèrent droit au chemin qui mène à Bethsamys; elles ne quittèrent point la voie, tirant avec effort, sans dévier ni à droite ni à gauche; les chefs des Philistins les suivirent à distance, jusqu'aux confins de Bethsamys.
13 A lokacin kuwa mutanen Bet-Shemesh suna girbin alkamansu a kwari da suka ɗaga ido suka hangi akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi farin ciki ganinsa.
Or, ceux de Bethsamys moissonnaient les froments dans la vallée; ils virent l'arche du Seigneur et ils coururent pleins de joie au-devant d'elle.
14 Keken shanun ya zo filin Yoshuwa a Bet-Shemesh ya tsaya a gefen wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun suka miƙa shanun hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
Et le chariot entra dans le champ d'Osée de Bethsamys; les hommes dressèrent auprès de l'arche une grande pierre; ils fendirent le bois du chariot, et ils offrirent les vaches en holocauste au Seigneur.
15 Lawiyawa suka saukar da akwatin alkawarin Ubangiji tare da babban akwati mai siffofin zinariya na ɓeraye da marurai suka ajiye su a kan ƙaton dutse. A wannan rana mutanen Bet-Shemesh suka miƙa hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu ga Ubangiji.
Ensuite, les lévites soulevèrent l'arche du Seigneur et la cassette avec les objets d'or qu'elle contenait; ils les posèrent sur la grande pierre, et les hommes de Bethsamys, ce jour-là, firent des holocaustes et des oblations au Seigneur.
16 Shugabanni biyar na Filistiyawan nan suka ga duk abin da ya faru, suka koma zuwa Ekron a ranar.
Les cinq chefs des Philistins les ayant aperçus, retournèrent à Ascalon le jour même.
17 Waɗannan su ne siffofi marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin miƙa hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron.
Voici d'où venaient les anus d'or que les Philistins donnèrent à cause de la plaie du Seigneur: un d'Azot, un de Gaza, un d'Ascalon, un de Geth et un d'Accaron.
18 Filistiyawa kuma suka aika da siffofin ɓeraye biyar na zinariya. Yawan ɓerayen sun yi daidai da yawan garuruwan sarakunan nan biyar na Filistiyawa. Garuruwan sun ƙunshi waɗanda aka gina katangar birni kewaye da su, da kuma ƙauyukansu. Babban dutsen da suka ajiye akwatin alkawarin Ubangiji, ya zama shaida har wa yau a filin Yoshuwa a Bet-Shemesh.
Et les rats d'or étaient en même nombre que toutes les villes des Philistins soumises aux cinq chefs, depuis les villes fortifiées, jusqu'au village du Phérézéen et à la grande pierre sur laquelle on posa l'arche de l'alliance du Seigneur, dans le champ d'Osée le Bethsamite.
19 Amma Allah ya kashe waɗansu mutum saba’in na mutanen Bet-Shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawarin Ubangiji. Mutane kuwa suka yi makoki domin Ubangiji ya hallaka mutane da yawa.
Parmi les hommes de Bethsamys, les fils de Jéchonie n'eurent point à se féliciter parce qu'ils regardèrent l'arche du Seigneur, qui frappa à mort soixante-dix de leurs chefs, outre cinquante mille hommes. Le peuple fut plongé dans le deuil parce que le Seigneur l'avait frappé d'une très grande plaie.
20 Mutanen Bet-Shemesh suka yi tambaya suka ce, wa zai iya tsaya a gaban Ubangiji Allah Mai Tsarki? Wurin wa akwatin alkawari zai je daga nan?
Et les hommes de Bethsamys dirent: Qui pourra aller et venir en présence du Seigneur, du Dieu saint? Chez qui, en nous quittant, ira l'arche du Seigneur?
21 Sai suka aiki manzanni zuwa Kiriyat Yeyarim suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawarin Ubangiji, ku zo ku ɗauka ku kai wajenku.”
Et ils dépêchèrent des messagers aux habitants de Cariath-Iarim, disant: Les Philistins ont rendu l'arche du Seigneur, venez et emmenez l'arche avec vous.